BABI NA HANSIN

4.3K 392 30
                                    

Da sauri Saif ya ɗago kai daga daga gurin da yake zaune ya kalli upstairs,

“Lafiya.?”

Ya tambaya yana kokarin aje magazin ɗin hannunsa ya tashi ya nufi upstairs ɗin yana cigaba da tambayar ta, bata faɗa masa gaskiya ba sai ta canja maganar,

“Wata na gani gurin windo”

Kunna kai yayi cikin ɗakin yana dube dube. ganin bai fahimci abunda take nufi ba

“Ba fa a ɗakin ba ta waje a windo na ganta”

Windo ya nufa ya shiga dubawa, shikan bai ga komai ba sai kawai yaja windon ya rufe, ya juyo yana faɗin

“Ina jin ita cen dake waje ne kika ango iska ne ke kaɗasu kinga garin akwai hadari, kuma kin bar windin buɗe amman ai kinga babu yadda za'ayi wai ya iya haurowa ta wannan windon tun da ba kasa yake ba”

Ita dai tana tsaye a bakin kofa rumgume da Lil Minal,

“Ba komai kiyi addu'ah ki kwanta”

Kai ta ɗaga masa ba dan ta yarda ba komai ɗin ba, har ya fice a bakin kofar take tsaye sai wani abu take da fuska kamar mai shirin yin kuka, can taji ba zata iya jure wa ba, ta juyo ta sauko downstairs.
   Ba kowa parlour sai tv dake ta aikinsa, haka ta zauna sai kalle kalle take kana ganinta kasan babu natsuwa a tare da ita, sai a jiyar zuciya take saukewa, tana haka Saif ya fito sanye da jallabiya dark blue,

“Gate na dawo mikike so a siyo miki?”

Ya faɗa daidai lokacin da ya karaso kusa da ita

“Bana bukatar komai”

Ta faɗa kamar bata son magana. Sai da ya kai bakin kofa sannan ta ce

“Please karka daɗe”

Juyowa yayi yana murmushi,

“Tunda kina jin tsoro ko.?”

Kasa kasa ta kalleshi ta ɗauke kai. Shi kuma ya fice yana cigaba da murmushin.
     Aiko kamar kar ya fita wani irin tsoro ya kara rufeta, ta rumgume Lil Minal a kirjinta gam ta rumtse ido, jin Lil Minal ɗin na motsi yasa ta buɗe idonta ta ajeye ta saman kujera tasan rumgunar ce wata kila bata so, tashi tayi da nufin kashe tv saboda karar da tayi yawa, sai kawai taga an kashe tv ba tare da ta karasa gurin ba, aiko ba shiri tayi baya baya tana haki.

“Ashe ki baki da amana Kairat? saboda zaki aurar min miji? kin yaudare ni cin cuce ni Kairat kuma ba zan taɓa barinki cikin kwanciyar hankali ba matuƙar kina cikin gidan nan”

A gefenta taji maganar tana juyowa ta ganta cikin bakar siffar da ta saba ganinta, wata mahaukaciyar kara ta saki ta faɗi kasa tana ja da baya sai uhun take ba kakkautawa, aiko sai bin ta take tana son kamota Kairat na ganin ta kusa karasowa kusa da ita ta kara sakin wata irin kara. jin an taɓa ta ta baya yasa ta rika numfashin a jure kamar zai ɗauke

“Nine Kairat ni ne”

Ina! tayi nisa bata jin me yake faɗi sai kaiwai ta cigaba da ihun jikinta na rawa, juyowa yayi ta ganta yasa bakinshi cikin nata ya rike kanta gam, sunyi minti goma a haka sannan hankalinta ya dawo ganin hakan yasa ya sake mata kai ya cire bakinshi daga nata ya rika kafaɗunta yana girgizata,

“Kairat”

Bata iya amsawa saboda numfashinta har yanzu rawa yake,

“Close ur eyes”

Da sauri ta rufe idon kamar mai jiran umarni

“Relax, relax ur body”

Ba musu tayi yadda ya umarce ta

BABBAN GOROWhere stories live. Discover now