BABBAN GORO.
NA
KHADEEJA CANDY
Candynovels.wordpress.com
WATTPAD @khadeeja_candy
Kainuwa Writers Association
*23*
Ido a rufe ya isa Asokoro villa, dan yau so yake yaji wace munafurka qanwarsa ce tayi masa wannan wawancin,
Sallama ma dan ta zamo masa dole ne kawai yayi ta.
Kallo ɗaya Momi tayi masa ta gane yana cikin ɓacin rai,
“Momi ina wuni.”
Ya gaisheta ne yana kokarin zaunawa saman kujerar dake fuskantar ta ta,
“Lafiya kalau Saifullah ya gidan?”
“Lafiya kalau Momi ina su Safiya.?”
“Suna ciki lafiya dai.?”
Bai ɓoye ma Momi komai ba, akan Minal da kuma abunda tace Kanwar tasa tazo tace mata,
Kai Mummy ta girgiza,
“Amman basuyi tarbiya ba, ina ruwansu da ita Safiya Rukaiya Lubna”
Momi ta kwala musu kira, ba ɓata lokaci suka fito suka zauna suna gaida Saif,
Bai amsa ba sai kawai yace,
“Cikin ku wacece taje gidan su Minal?”
Kallon kallo suka rik'ayi da junanasu zuwa can Safiya tace,
“Nidai ba ni bace”
“Toh wacece.?”
Ya tambaya a tsawa ce, nan kuma kowa yayi shiru, Momi ta kalleshi,
“Ita bata faɗa maka ko wacece cikin su ba.?”
“Ae ita ai bata sansu ba tace wadda ta faɗa mata dai fara ce kuma tace ita kanwata ce”
“Wannan ba hujja bace tunda dukansu fararene”
Faɗar Momi tana kallonsu, Saif ya fusata sosai
“Wallahi ko wacece ta faɗi kanta kamin na gano ta dan wahala kawai zata sha”
“Nice Yaya”
Tana faɗa ta koma gefen momi, tana kallonsa
“Toh uban waya aikeki”
Ta ɗan ɓata fuska,
“Amman Yaya ya za'ace wannan yarinyar kake so fisabillillahi yarnya nan fa bata da Uba kuma shaye shaye take kuma ance yar iska ce”
Kamin yayi magana Momi ta rigashi,
“amman Safiya baki da hankali toh ina ruwanki da ita ba shi ya ganta a haka yace yana so ba”
“Amman Momi jifa harda yan jarida sai buga labarin suke ai ana son idan mutun zaiyi aure ya auro yar mutunci yarinyar nan fa yar iska ce kuma bata da uba”
Momi ta fusata,
“Idan yar iska ce sai me! da ake ɗauko karuwa fa a gidan karuwai a sata bara'ah a aureta balle wannan da take karkashin iyayenta, Kuma ke kika maganar bata da uba shin ita ta halinci kanta ne ko kuma iyayen nata sun shawarce ce ne da zasu aikata ni mutane auna bani mamaki sai a rinka cewa yarinya shegiya shin ita tayi kanta ne ke zaki aureta ne ko ke zaki zauna da ita ne?”
Kuka ta shiga rerawa irin na marasa gaskiya, Saif dai baice komai ba dan Momi ta biyashi, daman yasan bada saninta taje gidan ba.
jin tana kokarin maida kukan na gaske yasa shi katsa mata tsawa,
“Wallahi zan dake ke duk ba ki bar nan gurin ba”
Da gudu ta tashi ta nufi hanyar ɗakinsu, Rukaiya da Lubna suka rufa mata baya.
Momi ta kalleshi cike da natsuwa tace
YOU ARE READING
BABBAN GORO
RomanceNOT EDITED ⚠️ "Kayi kuskuren fahimta Saif, babu soyayyarka a cikin zuciyata ko kaɗan" Kara matsowa yayi kusa da ita, ta yadda tana iya juyo bugun zuciyarsa, yace "Ki kalli kwayar ido na ki faɗa min baki sona ki karya ta kanki da kanki indai har da g...
