BABI NA ARBA IN DA HUƊU

3.7K 312 9
                                        


Har a kayi sadakan bakwai Mummy bata runtsa ba ko sau ɗaya, yadda take ganin rana haka take ganin dare gaba ɗaya bachi yayi kaura daga idonta tunanin Minal ya hanata sukuni duk ta bi ta canja ta koma wata kalar mace.
       Kairat kan abun ya zame mata biyu kewar minal ga kuma damuwar da Mummy take ciki, sai abun ya taru yayi mata tsaye musamman na Mummy da ita take gani yanzu, dan tasan Minal ta tafi inda ba zata taɓa dawowa ba.

   Ajiyar zuciya ta sauke ta tashi daga kwancen da take ta sauko saman gadon ta nufo downstairs, a hankali take takawa har ta sauko. a kujerar dake sitting room ta hango mummy zaune ta kafe idonta da wani diary dake hannunta, karasawa Kairat tayi kusa da ita ta zauna, sai a lokacin ta lura da Album ne ba diary ba.
    hannu tasa ta karba ta buɗe cike da son sani me ke ciki. hoton farko data fara gani shine na Minal tana rumgume da Mummy tana dariya! da sauri ta rufe album ɗin tana haɗiyar yawu, Mummy ta kalleta tana murmushi mai wuyar fassara

“Kin san abunda yafi damu na?”

Kai Kairat ta girgiza idonta cike da hawaye

“Minal bata taɓa ganin Familyna ba she's always like Mummy yaushe zaki kaini na gansu, yaushe zasu zo su ganni.... na kan faɗa mata ke kaɗai ce family na Minal ke zaki sake ginani kiyi min family na zama kamar kowa yanzu kuma ta tafiyar ta.....”

Dago kai Kairat tayi ta kalleta, hawayen da ta gani a idonta sun sata farinciki, don rabon da taga hawayen Mummy tun bayan an kawar da Minal, ko bata faɗa ba tasan kukan zuci ne take wanda yafi na fili haɗari.
   kara matsowa tayi kusa da ita tasa hannu tana share mata hawaye

“Kar mutuwar Minal tasa ki karaya Mummy I believe kema zaki yi naki family kinsan Minal ta bar miki baya kuma nima ina nan, Mummy kar tunanin baya ya hana ki tunani gaba”

Kallonta Mummy tayi still tana hawaye

“Ba zan bari ya zame min ciwo ba saboda sune suka guje na suka wulakanta ni mahaifina na cikina ya kasa ya fahimce yayi min uzuri akan abunda ba da son raina aka aikata shi ba basu cancanci zama dake ba Minal sunce ba zasu karɓe ki ba...”

Jinginawa Kairat tayi da jikinta tana faɗin

“Na sani ko ba daɗe ko ba jima sai sun dawo nemanki sai sun zo gareki Mummy kuma sai sunyi nadamar abunda sukayi miki”

Rumgume ta Mummy tayi tana girgixa kai

“I don't need them”

“Yes Mummy we don't need them”

       Sun daɗe a haka kamin Kairat ta ɗago ta kalleta

“Mummy me kike so ki ci?”

“Komai bana bukatar komai....”

Bata fuska tayi ta tashi ta nufi upstairs tana kuka, da sauri Mummy ta kalleta mi kuma yasa ta kuka yanzu mi akayi mata? tashi tayi ta bita tana tambayar ba'asi,
   Har ɗaki Mummy ta bita, tana kokarin kwanta saman gado ta rikota

“Lafiya Kairat mi a'kayi?”

Batayi magana ba sai cigaba tayi da kuka, hankalin Mummy duk yabi ta tashi nan take ita ta fashe da kuka, ganin hakan yasa Kairat ta tsagaita nata kuka ta shiga share hawaye, mummy ta rika fuskarta

BABBAN GOROMga kuwentong kahuhumalingan mo. Tumuklas ngayon