Page nine

54 6 0
                                    

Typing~~~~📱

*© HIKIMA WRITERS ASSOCIATION*

'''(home of peace,joint of entertainment, to educate and enlighten our readers)

   🌼 *Saboda* *duniya* 🌃

Writing by......
<<<<≤<≤<<<<<<<<<<<<
*Annafie*💗

07051376476

Nafeesa A Guga @ wattpad

*bismillahir rahman  rahim*
Page 17⏩18
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
Dukan nin su jiki a sanyaye suka shiga mota xuwa part din yarima har suka iso babu wanda yace da wani kala a parlor suka zauna sae shigo ake ana gaisar dasu...
Bayi ne suka fara shigo masu da  abinci. suna ajewa ...  Sae da suka gama snn aunty fati tace su sauko suci abincu... Kodaya khadija bata jin dadin abincin  sai juya spoon take maganganun Dada suna mata yawo a tsakkiyar kai aunty fati na lura da ita amma sae bata ce komai ba.. Har suka gama kowa da abinda yake sakawa a zuciyar sa... Saeda suka gama snn aunty fati ta kamo hannun khadija tace "kanwata ni xan tafi saeda safe kuma ga Rahma nan zata rinka tayaki kwana ko zaki iya kwana ke kadae... Da sauri ta girgixa kai kanta a kasa... Murmushi aunty fati tayi kafin tace to shknn mu kwana lpy tashi tayi suka bita a baya a bakin kofa khadija ta tsaya suka fice itada Rahma daxata dauko kaya ... Khadija ta dawo cikin parlorn tana dan binsa da kallo kafin ta haye sama Saeda ta dan tsaya tana kallon corridor din mai dauke da kofofi har hudu duk da tata kafin ta shege bedroom din shima kallon ko ina take komai na dakin mai kyau ne kayan jikin ta ta fara ragewa kafin ta shige wanka tana fitowa ta samu Rahma zaune saman gado tana danna wayar ta murmushi ta sakarwa khadija tana fadin "matar yayan mu" khadija tayi murmushi kafin tace "amma dae kin rufe mana kofa ko dan wlh tsoro nake ji" dariya Rahma tayi kafin tace "haba karki ban kunya nata matar soja da tsoro yayana fa jarumi ne" khadija ta nufi mirror tana murmushi batace komai ba.. Rahma ta tashi ta bude wardrobe ta dauko mata sleeping wears snn itama ta shige toilet din.....
Koda rahama da fito can karshen gado tasamu khadija tayi tagumi ki kayan bata saka ba daga ganin ta tana cikin damuwa  dan har Rahma ta karasa inda take bata sani ba... Cire tagumin Rahma tayi kafin tace "kina kewar gida ne" murmushi kawae khadija tayi kafin ta gyada kanta.. Rahma ta dan dube ta cikin sanyin murya tace "Abinda umma ta maki yana damunki har ynx ko?" Da sauri khadija ta girgiza kainta dake kasa tana wasa da yatsun... Rahma ta zauna gefen ta a hankali tace "aunty kiyi hakuri haka halin umma yake dan baewae kece bata so ba tsanar da tayiwa ya Ammar ce ta shafeki dan gaba kodaya umma bata kaunar mu a cikin gidan nan... Da sauri khadija ta dago cikin mmki tace "meyasa to" boyayyar aziyar zuciya Rahma ta sauke kafin tace "sbd ba itace ta haife mu ba batason ganin mu a gidan nan sbd ba kamar ya Ammar saboda duniya ta dauki tsana ta daura mana kinga ki zama nan bamu cika yi ba muna tare da mom dinmu a can misra dan mahaifin mu da yan uwan mu kawae yasa muke yawan zuwa nan ta kwashe duk lvrn" ta karashe tana goge hawaye khadija ma kukan take meyasa sbd neman duniya zaka takura wa rayuwar wani da kyar khadija tace Allah yasa dae mudace" Rahma tace ameen snn ta mike xuwa ina kayan ta suke ta dakko ta saka suka kwanta... Khadija kam kasa bacci tayi tananin Dada "knn ynx da zata samu wata hanya zata iya halaka Ammar .. Furzar da iska tayi lallai gara yan gidansu tindasu hassada ce kawae baxasu iya kisa ba shikuma dadin sa daya yan uwansa wanda suke uba daya ba kinsu... Sai sake sake take a haka har bacci ya dauke ta.....
Suna yin sallahr asuba suka koma bacci har kusan 10 basu tashi ba dan kowane da gajiya a tare dashi... Rahma ce ta tashi tabi khadija da kallo yanda take bacci hankali kwance bata tashe ta ba dan tasan kila a gajiye take wanka Rahma tashiga bata wani jima ba ta fito har lokacin bata tashi ba .... Wayar Khadija ce ta fara ringing dan guntun tsaki Khadija tayi kafin ta duba ganin number ce yasa  ta kyale wayar tacigaba da baccin ta Rahma tace "tab bacci yayi dadi gsky" kiran ta aka karayi tashi zaune khadija tayi tasaka wayar a silent ta dubi Rahma da saki baki tana kallon ta" Khadija tace "wae har kin tashi" murmushi Rahma tayi kafin tace "morning Aunty" "khadija tace "morning ya gajiya" "Alhmdllh kema naga kina cikin ta wnn bacci haka.. Ko call baki dauka" cewar Rahama.. Khadija ta yamutsa fuska "wlh bana so a kirani ina bacci and is unnamed number fa" dariya Rahma tayi kafin tace "lallai kam kamar ya Ammar knn but shi idan ya kiraki ko westing tym kikai baki dauka ba kin bani wlh... " shiru Khadija tayi tana kallon Rahma..... "Srry ko kinji haushi ne" khadija ta harare ta Rahma ta kara fashewa da dariya kafin ta fice a dakin.. Murmushi khadija tayi kafin ta shiga toilet tayi  wanka.. Tana gama shiryawa  taji ana danna door bell a kasa .. Tashi tayi ta sauka kasan ta bude a tunanin ta Rahama ce tana budewa sae taga wasu mata su shida kowace hannun ta dauke da kayayyakin da alama breakfast ne... Zubewa sukayi suna gaishe ta.. Duk sae taji wani iri gashi dae a girme sun girme ta amma sun durkushe a gaban ta duk sae taji wani iri da sauri tace "dan Allah ku tashi mun kwana lpy cikin  jin dadi suka ce "lpy lau dama gimbiya fati ce tace mu kawo maki abin  kari snn mugabatar maki da kanmu a matsayin bayin da zasu rinka maki hidima" to ku shigo Khadija ta fada tana kokarin tayasu shigo da kayan da sauri sukace "ki gafarcemu Rankiya dade wnn aikin mu ne" duk yanda taso ta karba basu yarda sun bata ba... su suka shiga dashi ciki suka jera a dining tana zaune tana kallon su har suka gama suka xo zube a gaban ta kowace ta gabatar mata da kanta daga nan sukace ko da abinda za'a maki ne ranki ya dade kafin Khadija tace wani abu.. Rahma da tashigo ynx tace kuje dakin ta zaku gyara tunda duk an gyara nan ... Da sauri Khadija tace "no just let them go dan har na gyara ma" sallamar mu Rahma tayi suka fice... Aunty fati ce tashigo tare da  Sameera.. Aunty fati ta zauna tana fadin wae baku fara breakfast din ba.. Khadija ta zame kasa kanta kasa tace "Anty fati ina kwana" da sauri aunty fati ta daga ta zuwa saman kujera "kanwa ta kintashi lpy ya bakunta" "lpy qlw Alhmdllh aunty" Khadija ta fada kanta a kasa tana wasa da yatsun ta... Kafin ta dubi sameera tace "ina kwana" zaro ido sameera tayi kafin tace Rufamin  asiri wlh ya Ammar yaji kina gaishe ni dani dake zai hada yy maganin mu dan ke Aunty na ce... Morning aunty kin ta tashi lpy" kasa kawae tayi da kanta tana murmushi" aunty tace ku tashi muje muyi break.. Tashi sukayi  zuwa dining sameera ce tayi serving din kowa abinci ne mai rai da lpy sae kamshi yake.... Walid ne ya shigo rike da Shaheed... Ware idanu yy yana kallon su kafin yace "good kace kuna nan ni kun share ni ko kuna nan da auntyn mu kuna break ni kadae ne babu and nobody cares to sae naci.. Muje kaji boy" yaja shaheed zuwa dining din ... Walid har da wani dukawa yace "morning auntyn mu kin tashi lpy" kasa amsawa khadija tayi ganin yanda ya wani duka mata gashi a shekaru  ya kusa yaya mujaheed" murmushi kawae tayi kafin ta kamo hannun shaheed da shima yake gaisheta tace "come and have break by boy" walid yace "toh.. Nine baxaki amsa gaisuwa ta ba ko to wlh kuyi sheda na gaishe ta dan nasan ya ya Zae iya kwado dani idan yaji bn gaishe da matar sa.. Aunty, da sameera kuxama witness dan nasan halin Autar Abie" turo baki Rahma tayi "nide bnji sanda ka gaisheta ba aida ka gaisar da ita da ta amsa... Sakin baki walid yayi kafin yace "to shknn idan ya dawo ki fada masa I can escape because I have to witness kinga he'll punish you sbd kin masa karya and bayan nan i'll tell him what happened dat day..." Da sauri tace "kai ya walid kar muyi haka da kai ni cemaka nayi zan fada" dariya yy yana zuba ma kansa abinci sameera tace "wlh har na hango kwadon da yaya zaeyi dake a gidan nan.. " Khadija dae najin yanda suke magana  akan wanda akace mijin ta amma bata ce komai ba abincin ta kawae take ci tana bama Shaheed... Walid yace wae Aunty Amarya ke kadae kk kwana part din nan" Aunty fati tace "tare da Rahma suka kwana" dariya Rahma tayi kafin tace "kai aunty Khadija a kwae tsoro wae cewa tayi da babuni baxata iya kwana ba harda su cewa na rufe kofa" hararanta Khadija tayi... Walid yace "kina matar maxan fama kikeda tsoro" Rahma tace "that's what i told her" "nima yau nan zan kwana" gyada kai walid yayi kafin yace "lallai kam kuyi kwanan ku san ranku kafin yaya ya dawo shigowa ma ya gagare ku.... Aunty fati tace "wlh kau.  and daga yau non of you should called her aunty Khadija again because   sunan granny's din mu ne both mummy and Abbie let her be aunty HANAN ai hakan yy ko" "that's nice aunty" cewar Sameera  Walid yace "I wish ni na fara kawo this idea because nasan Abbie da mummy har kyauta  sae sun mun amma duk da hakan i'll be the first to gist  Abbie  dan nasan xan samu wani abu...
Kafin ya mike Rahma ta tashi da sauri ta fice tana fadin saena riga ka... Walid yabi kofar da ta fice da kallo kafin yace "wlh nariki autar Abbie baxan mata da kyau ba bari nakira mummy a waya kafin tarugani yana fadin haka ya masu sallama yafice sameera na bin bayan sa tayi tana dariya.. Khadija ma dariyar take dan Rahma ta bata dariya dan fira sukayi da aunty fati kafin itama ta fita ta barmata Shaheed da tuni yy bacci a jikin ta sama ta haye da Shaheed xuwa bedroom dinta  ta kwantar dashi  itama ta kwanta yayinda takejin yaran sarkin sun birgeta sun hada kansu kamar ciki daya suka fito kowane na kaunar dan uwansa dukda kan iyayensu ba hade yake ba akasin yan gidan su da suka tsane ta kamar ba jininta ba sbd wani dalili mara amfani.. Kallon fuskar Shaheed tayi yaron kyakkyawar kamar maman sa da yan uwanta dan duk cikin su babu wanda zaka kalla baka kara ba... 
  Walid na fita yakira numbern mummy ya fada mata sunan da aunty fati tace su rika kiran Khadija dashi sbd ita da Abbie.. Cikin farin ciki mummy tace "ai kam dole ne na bata kyau ta.. " marairaicewa walid yy kafin yace "mummy nifa dana maki albishir" dariya mummy tayi kafin tace "ai dole na maka kyauta mai tsoka" "mummy nima dan tare mukayi shawarar da aunty... " kafin ta karasa walid ya bige bakin" mummy karya take rani zata saka min" yana gama fadin haka ya kashe wayar yana hararan sameera kafin ya shige part din Dada itama bayan sa tabi... A parlor suka iske Dada suna lvr da kausar.. Dukawa sukayi suka gaisheta  ta amsa kafin tace "meya hanaku zuwa kuyi break fast tin daxu" "no umma dont bother munyi tare aunty Hanan dasu aunty fati..."cewar walid Ya mutsa fuska tayi kafin tace wace kuma" sameera ce tace "umma Amaryar ya Ammar" wani wawan kallo hajja ta rinka binsu dashi kafin tace "wae ku sae yaushe zakuyi hankali ne sauna zan yanke alaka tsakanin ku da Farha da yaran ta shine ynx tsabar kaskantar da kai zaka tafi wajen shegiyar can da aka lakaba masa harda wani ce mata aunty kana dan sarki zaka cema yar talakawa aunty..." Kausar ta fashe da kuka wlh sae naga bayan yarinyar nan duk da nasan Ammar baxae taba sonta  ba.. Tana fadin haka ta shige bedroom.. Walid yace "umma sufa yan uwana ne taya zaki yanke alaka tsakanin mu kuma matar yarima aunty na ce no matter how and I see nothing there dan nace mata aunty kuma I have to love her yanda xanso dan uwana... Rufe mun baki shashashan yaro bakada wani dan uwa da ya wuce sameera kai ko kishin kan ka ma bakayi.. Kai yakamata ace kana ruling Kingdom din nan ba Ammar ba kai ne uwar ka da uban ka duk yan masarautar nan idan Ammar ya amshi sarautar nan danging mahaifiyar sa ne suka samu kama ta yy kafito ku gwabza dashi kanuna masa kai kafi can can ta bashi ba dayake ganin yafi kowa har yake mana kallon bamu kai ba ka sauke masa duk wani jida kansa ka nuna masa bafa shi kadae bane jinin sarauta...." Wani murmushin ta kaici walid yy kafin yace "umma knn Ammar dae dan uwa na ne kuma shiyafi can can ta da yaxama yariman masarautar nan danni..". "Dallah rufe mun baki mara zuciya kawae wanda baya kishin uwarsa wlh farha tariga ta shanye min ku in banda haka ina mahaifiyar ku har ina fada kuna fada su yaran ta kun tabaji sunyi mata gaddama  sae ni da baku kauna ko zaku tashi ku fice min anan koko" ficewa sameera tayi tana tura baki yyinda walid yace "Allah ya huci zuciyar umma" snn ya fice dunkule hannun ta tayi ta buga a dayan tana zagaye dakin "wlh na tsani Ammar kuma saena kawo karshen sa... Dan baxan taba yarda sarauta ta koma hannun su ba.. Kuma baxan taba bari ya kusanci matar sa ba bare har ta samu kwae dan inhar hakan ta faru to nashiga uku ...., zan iya yin komai SABODA DUNIYA dole nabi ko wace hanya dan na salwantar da rayuwar su shida wnn talakar matar tasa wnn ALWASHI NE..  
More comments more typing... ✍️
*#VOTE*
*#SHARE*
*#COMMENTS*

✨✨✨
*NAFEESA A GUGA*
😍😍😍😍😍😍😍

SABODA DUNIYA Where stories live. Discover now