P31

426 21 0
                                    

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*

 

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *31*

'Karan da yayin ne ya janyo hankalin mu gaba 'daya, Ammi da dama take kan hanyar zuwa gurin Alhajin sai tayi saurin 'karasawa ciki.

A rikice ta shigo tana tambayar Alhajin " me ke faruwa?"

Alhaji Baba ri'ke yake da hannun Deen yana 'ko'karin kwantar masa da hankali amma ina sam ya rasa nutsuwar sa.
    Jin muryar Ammi da yayi ne ma ya sanya shi 'karfin halin mi'kewa cikin idanun sa cike taf da ruwan hawaye ya tsaya gaban Ammi.

Hannun ta na dama ya kamo ya 'daura saman 'kirjin sa saitin zuciyar sa yace " Ammi...kiji bugun zuciya ta, kiji irin 'ka'k'karfan soyayyar da nake yi mata...Ammi dan girman ki tausaya min kar kice min dagaske ne Amina ta rasu...Nanne ta tafi ta barni Ammi dagaske ne...?"
Sai yanzun hawayen sa suka gangaro kan kuncin sa, yana jin hakan amma bai kula ba still hankalin sa na wurin Ammi yana sauraran jin amsar bakin ta...Ammi kam duk jikin ta yayi sanyi bata ma san me zata ce da shi ba, bata san abin nasa har haka ya girmama ba, Muhammad 'din ta ne yau yake kuka da hawayen sa, kuma kukan ma akan mace.
Tsura masa idanu tayi tana kallon sa, tausayin sa na sake ratsa ta ji take tamkar ta taya shi kukan itama, amma tasan yin hakan tamkar ta fallasa asirin zuciyar ta ne.
     Ganin kamar yana 'ko'karin sulalewa 'kasa ne ya sanya Alhaji saurin 'karasowa ya tallafo shi wanda sai a lokacin Ammi ma ta ankara da hakan a firgice ta ambaci sunan shi tana tallafan 'daya gefen nasa.

Kai Mu'een ya girgiza mata idanun sa lumshe batare da ya amsa sunan shin da ta 'kira ba kawai ya fara fa'din ..."..me ya..sa..zaki tafi..ki barni?...Ammi me yasa...bata jira na dawo na sanar da ita 'dumbin soyayyar da na ke yi mata ba..."

" Haba Muhammad kai fa musulmi ne, me yasa kake fa'din irin wa'dannan kalaman...bacin kasan Allah ne ke da mutuwa ba mu ba".
Alhaji Baba yayi 'karfin halin fa'din hakan yana gyara masa kansa dake jikin sa.

Wasu hawayen ne suka sake gangaro masa da gudun su...idanun sa ya bu'de ya tsayar cak akan fuskar Alhaji Baba bakin sa na rawa da alamar magana yake son yi amma ya kasa saboda azabar dam'kar da zuciyar sa tayi masa da 'kyar ya iya fuzgan " Alhaji...dagaske....ta barni...?"
Kafin Alhaji yayi wani yun'kuri sai gani yayi Mu'een ya mi'ke sumamme a jikin sa.

Ammi kam tuni ta fara kukan itama cikin ranta take fa'din " wannan wani irin masifa ne?"
Ganin yanda ya mi'ke ne ya sanya ta rikice tafara fa'din _innalillahi wa inna ilaihi raji'un_ ... _Alhaji me yafaru what's wrong with him..?"_

     Cikin sanyin murya Alhaji Baba yace " ki kwantar da hankalin ki please...ba wani abu bane he just fainted".

Yana shafa cikin hannun Yah Deen ya fa'di hakan batare da ya kalli Ammi ba...shi kansa ya kasa nutsuwa gaba 'daya hankalin sa ya tashi, dama irin abinda tuntuni yake gudu kenan shiyasa ma ya kasa sanar da shi tun farkon faruwar lamarin.

  Ammi na jin cewa suma yayi ta tashi da sauri ta 'debo ruwa tana 'ko'karin she'ka masa Alhaji Baba ya dakatar da ita.
Da mamaki tace " me yasa kuma Alhaji...idan ansa masa ruwan zai ta shi ai".
Kai Alhaji ya girgiza mata sannan ya bu'kaci ta bashi wayar sa.

Wayar ta 'dakko masa yayi 'kira inda ya bu'kaci ganin wani likita dake unguwar tasu ya kuma sanar dashi abubuwan da yake so ya zo dasu sannan ya cire wayar daga kunnan sa ya ajiye ta gefe.

NOORUL✔️Where stories live. Discover now