P70

499 44 4
                                    

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*
 

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

_*Daga marubuciyar Littafin CAPTAIN ABBAS*_

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *70*

Tun zuwan mu kuwa har yau ban ta6a zuwa Shuwarin ba, Yah Deen shi ka'dai yake zuwa ya dawo abin sa, duk yanda nake nuna damuwa ta  akan son tafiyar amma baya kulani ya kan je ya kwana 'daya tak ya dawo.

Duk bayan tafiyar ta sa kuwa kuka nake yi sosai abu na saboda tsananin son zuwan da nake yi.

Gashi abin haushin ko yaje ya dawo bana samun jin wani labari daga bakin sa abinda yake gaban sa kawai yake cigaba da yi...

Duk yadda nake 'kaguwa inji yace min su Ammi sunce kaza, ko kuma Ummah tayi kaza...haka nake ha'kura domin Yah Deen baya bani labarin komai, ni kuma bana iya tamtayar sa.


*****
        Watannin mu takwas a garin Bauchi a lokacin mun yi nisa da fara zana SSCE, cikin 'dan hutun dake tsakanin Waec da Neco acikin sa  na fara fuskantan wasu sauyi tattare da lafiya ta.

Zazza6in dare, da kuma yawu da baki na ya fara yawan tarawa, abin sosai yake bani haushi har cikin zuciya ta...gashi bansan dalilin ba sam.

Da farko nayi tunanin Maleria ce ke damuna amm sai naga inba daren ba ba na sake jin alamun zazza6i ko wani abu sai dai ko yawun da yake 'dan takura ni wasu lokutan.

Da yake ba gida yake yini ba hakan yasa bai da labarin halin da nake ciki.

Ranar wata Juma'ah zai fita aiki da safe bayan har ya min sallama yana daf da fita daga parlour na 'kira sunan shi.
Cak ya tsaya sannan ya waigo, sai nace" Dan Allah idan zaka dawo ka siyomin magani kullum yawu damuna yake yi sai na nasa abu a baki na.

Kallo na ya tsaya yi batare da ya furta komai ba, yayin da cikin zuciya ta nake ayyana" Allah yasa dai ba 'kin siyomin zai yi ba".

Kawar da kansa yayi ka'dan daga kallona tamkar wani tunani a hankali kuma naga ya tako izuwa gaba na.

Fuska ta ya tsaya kallo kamar mai karantar wani abu.." Me ke damun ki?"
Ya sake tambaya ta as if bai ji me na fa'da da farkon ba.

Ban damu ba na sake maimaita masa cuz sosai nake so inga na daina wannan yawun.

" Bayan shi fa ba wani abu?"
Saurin girgiza kaina nayi.
Sai yace min" In 'dauko mayafina mutafi tare idan an duba ni sai in dawo gida".
Shi da kansa ma daman ya fahimci wani sauyi tattare da ni musamman na rashin sukuni a 'yan kwanakin kawai shiru yayi da tunanin in damuwa ce ke damuna ai da kaina zan fa'di.
               Sai kuma gashi hakan akayi, Yah Deen da kansa ya gwada ni bayan isarmu asbitin nasu.

Bayarwa yayi aka akai Lab shi kuma ya zauna tare da ni, kwata-kwata ma sai ya kasa yin aikin komai, har 'kiyastawa yake cikin ransa yanda zai ji idan hasashen ya zama gaskiya.

Ai kuwa sosai nayi mamakin sa, dan kuwa hauka ne ka'dai be yi ba ganin sakamakon gwajin da akayi min da abinda ke 'kunshe a ciki.
Wai ni Hudah ce ke 'dauke da ciki a jiki na.

Dama tunda yaji abinda na gaya masa da sukayi kama da symptoms in masu ciki sai zuciyar sa ta kasa natsuwa.

Lokacin da ya tabbatar cikin ne dagaske kuwa murna tamkar zai cinye ni, haka ya dinga bin jiki na kisses yana samin albarka da fara'ar sa...Alhamdulillah kawai yake ta faman maimaitawa cikin zuciyar sa.
Haka kawai bazata ya tsinci kansa cikin matsanancin son cikin jini da zuciyar sa.

NOORUL✔️Hikayelerin yaşadığı yer. Şimdi keşfedin