P39

507 26 1
                                    

💕 *NOORUL* 💕
(Haske nah)

By
*Salmerh MD*

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

🤞🏻

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *39*

" Ai shine ya sani sharar"!
Wannan karan ina share hawaye na nayi maganar.
" Waye?".
Ammi ta sake tambaya ta tana mai bada dukkan hankalin ta gare ni.
" Yah Deen 'din ?"
Na bata amsa hawaye na na sake gangarowa.

Salati Ammi ke zubawa da jin abinda na fa'di, tana tafa hannuwa tace "
Hudah dagaske shine ya saki shara?"
Da kai na bata amsa alamar " Erh"
Wannan karan Ammi baki ta ri'ke cike da mamaki tace" Allah Buwayi...Ina gidan nan ya akayi har yazo ya aikata hakan batare da na sani ba?".
Ina tura baki nace
" Ai ya da'de da fa'da min kuma yace kar ingaya miki in ba haka kashe ni zaiyi".

Dariya ma maganar tawa ta bata amma yanda Yah Deen ya ninke ta abaibai ya yaudaretan sai ya sa ta jin 6acin rai sosai, " Wato barazana yayi miki da kisa"
Ta fa'di a fili"..hmm lalle!... shiyasa ya daina neman atura masa kowa...munafiki ashe ya san munafurcin da ya 'kulla...zaizo ya same ni ai"

Ni kuwa ina daga tsaye sai goge idanu nake yi kamar zan cire su, a lokacin tsoro biyu ne suka ha'du min, ga na kar Ammi ta sashi ya zane ni ga kuma tunowa da nayi cewa ya hana ni sanar da ita wanda hakan ya sanya hawayen nawa kasa tsayuwa.

Zama tayi ta gyara tare da janyo hannu na zuwa gaban ta kusa da ita, kafin ta furya komai na 'dago jajayen idanu na sauke au kan fuskar ta nace " Ammi kar ki ce masa na gaya miki dan Allah cewa yayi kashe ni zai yi"
Na 'karasa cikin kuka.

...Cikin lallami da kwantar da murya tace
" Haba uwata ina nan din kike tunanin zai kashe min ke kuma in barshi, 'kyale ni da shi zai zo ya same ni ne...kinji?"
Kaina na 'dage alamar Erh naji.
" Yanzu gaya min me ya faru duk karki 6oye min kinji ".
....Daki-daki na hau bawa Ammi duk amsar tambayar da ta min.

Takaici ne sosai ya kama Ammi jin yanda tsawon lokaci yake wasa da hankalin ta kamar 'kwallo...ya muzanta ta ya nuna mata bata isa ba, sannan ya girgiza mata igiyar al'kawarin da ta 'dauka kafin ta kar6o Noorul Hudah da wani irin fuska yake so iyayen na su dube ta ?"
Ran Ammi sosai ya 6aci da shi.
Abinda kawai ta iya 'karfin halin furta min a fili shine" Rabu da shi zai zo ya same ni"!

Ni kam take sai na marairaice fuska tuno irin kashedin da ya zayyana min gashi na warware wa Ammi komai, cikin kuka da marairaita nace " Ammi dan Allah kar kice na gaya miki Allah kashe ni zai yi".

Dai-dai nan Zaidu ya shigo 'dakin yana ta6e baki jin abinda nake fa'dawa Ammi, shi haka yake sam bai damu da damuwar kowa ba har ma sai nake ganin gara kowa ma akaina, domin iya tsawon zama na a gidan bai mun sha'ku da shi ya fara yi min kallon 'yar uwa ba yayin da ni nake jin su tamkar 6angaren jiki na.

Daga can hanyar corridor Saif dake biyo bayan Zaidu yake fa'din " ...Wai Zaid anya kuwa ka tuna siyan wannan...."

Cak maganar tasa ta yanke sakamakon ganin yanda nake rusa kuka...Ammi ya kalla sai yaga itama hankalin ta na kaina.
Take akalar tambayar tasa ta canza daga kan Saif zuwa Ammi inda ya karasa shigowa parlourn da sassarfa yake tambayar.." Lafiya Ammi me ya same ta?"
Ammi bata tanka shi ba kawai ta cigaba da duba na...shi kuma Saif ya 'karaso ya zauna daga gefen Ammi yana min duba a tsanake da son karantar yanayin da nake ciki.

Ammi kuwa 'dan takaitaccen murmushin takaici ta saki gami da kamo hannu na tana share min hawaye tace " Ki kwantar da hankalin ki, ba na gaya miki ba, ai be isa ya kashe ki ba matu'kar ina nan kar ki damu kinji?"
Sai na 'dage kaina sama.
" Yauwa...sannan daga yau ki daina 6oye min abu kinji..koma miye ya faru kar ki 6oye min bana son irin haka ni...ko me ya miki ki zo ki sanar dani, zanyi maganin sa, yanzu wannan da kin gaya min tuntuni ai da hakan ba zai faru ba, da ba zan ta6a bari ya ringa bautar da ke ba balle har su lattin zuwa makaranta, munafukin kuma ya sani amma ya basar...zai zo ya same ni ne...ni ina nan na saki baki ina tunanin ramar girma ce ta kamaki ashe ba haka bane..wani abin ne daban...hmm yaron nan na wasa da ni Allah".

NOORUL✔️Where stories live. Discover now