P33

526 31 2
                                    

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*

 

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

🤞🏻😍 *Dedicated to 'kawa AMEEN D. ABDULLAHI...fatan Alkhairi 'kawar kirki...Allah ya 'kara dan'kon 'kauna* ~{Ameen}~ 🙏

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *33*

Ammi bata damu ba kawai ta daidai ta zaman ta tare da bu'de abincin ta sanya spoon ciki.

"..Ina yini?"
Na fa'di kaina 'kasa kuma batare da na ambaci sunan kowa ba...haka kuma in ce masa ya jiki ma sai ya min nawi a baki na.

Shima 'din 'dan ra'ayi kuma bai amsa ba, sai da Ammi tace da shi..."..da kai fa take".
Bai ko 'dago ya kalle ni ba ya amsa da fa'din " lafiya "a takaice.

Ji nayi duk babu da'di, duk da yake ma ba yau na fara gaishe shi yana amsan min a hakan cikin halin ko in kulan ba amma na yau 'din ka'dai sai naji na muzanta.

'Daga ido na nayi na saci kallon sa...yanzun ya 'daga kansa sama ya jingina da jigin kujerar hannun sa a 'kirjin sa idanun a kuma a lumshe...hararar sa nayi gami da kauda kaina gefe, cikin raina nace " wannan ko bashi da lafiyan ma ba zai canza hali ba".

Muryar Ammi ne ta katse min tunani na..inda naji tana fa'din" yauwa 'yan matan Ammi je kawo wa Yayan ki ruwa...amma ki duba ba mai sanyi sosai ba kinji?"
Kai na 'daga mata tare da juyawa sum-sum na fita daga 'dakin.

      Ina fita sai Ammi ta 'debo abincin ta nufo bakin sa da shi " open ur mouth".
Ta fa'di da yaren su, ganin ta kusanto bakin sa da abincin ne ya sanya shi bu'de baki batare da musu ba ya ansa.

      A hankali yake taunawa da'din abincin na ratsa shi, wanda ko 'kamshin abincin ka'dai ma ya isa ya ja ra'ayin mutun ga cinsa, doya ce da taji manja da bushashshen kifi harda kayan lambu...sosai yaji da'din abincin dan haka koda Ammi ta 'kara bashi be yi gardaman kar6a ba, lokacin da ta 'debo zata bashi ne a karo na uku har ya bu'de baki sai cak idanun sa suka sar'ke da nawa da isowa ta wurin kenan.

Bakin sa yayi saurin rufewa tare da yin 'kasa da idanun sa, a hankali sannan ya kai hannu ya kar6i spoon 'din daga hannun ta can 'kasan ma'koshi ya furta " Ammi let me..."
Ita ma Ammi ba ta hana shi ba ta sake mai tare da sakin murmushi, inda batare da 6ata lokaci ba ya 'karasa kai abincin bakin sa.

    Bai sake bi ta kaina ba dan ko inda nake bai sake kalla ba ya cigaba da cin abin sa cikin ransa yake tunanin ai idan yaran nan suka ga Ammi na bashi abinci a baki ai raina shi zasu yi....daga haka ya 6ige da tunanin kama da nake yi da marigayiyar sahibar sa.

A hankali na yi sallama tare da 'karasowa gefen Ammi na mi'ka mata cup da ruwan da na 'dauko...tana kar6a na juya na fita batare da na sake jiran komai ba.

   Ammi bata fito ba sai da tabbatar ya ci abincin tukunnna.
   Bai ma ci ko rabi ba ya ture gami da sanar da Ammi cewa ya ishesa abincin.

Ruwa ma ka'dan yasha ya ajiye.
  Ammi sosai taji da'din hakan dan haka da fara'ar ta ta fito da ragowar fuskar ta cike da annurin ganin jikin nasa Alhamdulillah sai godiyar Allah.

Har lokacin dawowar Alhaji Baba tayi Yah Deen bai fito parlour ya zauna ba, masallaci kawai yake fita da ya dawo kuwa sai ya wuce 'dakin sa, sai bayan sallar maghrib ne ma suka 'dan zauna da Alhaji can harabar gida har isha ya same su wurin, daga can suka wuce masallacin.

NOORUL✔️Where stories live. Discover now