P27

520 28 5
                                    

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*

 

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *27*

Da yamman ranar kuwa babu islamiya  da yake ranar Alhamis ne kuma bama zuwa, ranar ma ni da Nanne muka kai marka'den shinkafar wainar Ummahn mu...da kuma gya'da dayake yau d'in harda gya'da ta gyara shiyasa muka tafi mu biyu, dama ranar da duk za'ayi markaden gya'da ne muke tafiya mu biyu idan kuwa marka'da'd'iyar gya'dar Ummah bata kare ba ni ka'dai ke zuwa in marka'do mata shinkafa.

     A hanyar mu ta dawowa muna tafiya muna 'yar hira, wani sa'in kuma fa'da mukeyi da ita dan ni nawi ya dame ni sosai yayin da ita kuma take faman jan 'kafa tafiyar ta kamar dan dole take yin sa.

Burina tayi sauri mu wuce gida ita kuma ta'ki a hankali take tafiyar ta kamar yanda ta saba.

      Cikin shirin zuwa ball yazo ya gifta mu ban sani ba ko bai gane ni amma ni kam sau 'daya na kalle shi amma sai na gane shi.

   Sai da ya wuce ne sannan Nanne tace da ni " tab amma wannan yana da kyau gaskiya".

" Waye wai wancan ?"
Na tambaye ta gami da nuna shi da bakina cuz da duk biyun hannaye na ri'ke roban dake kaina.
Nanne sai tace " ehh mana koke baki ganshi ba "
Juyawa nayi na cigaba da tafiyata sannan nace
" Na ganshi mana... 'dan gidan Alhaji Baba ne, mugunta ce dashi ingaya miki sosai".

  Baki kawai Nanne ta ta6e bata 'kara magana ba, daga nan kuwa muka cigaba da tafiyar mu.

  Na kanyi gaba in barta dan yanayin tafiyar mu ba 'daya bane da ita sam...ban sani bama ashe Nanne kam hankalin ta duk ya koma kan Yah Deen ne, tafiya take tana waigen sa lokaci-lokaci....ni kuwa dake gaban ta bansan hakan ba sam....bazata kawai naji karan fa'duwan abu...waigowata kawai sai naga ashe marka'den dake kan Nanne ne ya kife gaba d'aya sanadin tuntu6e da tayi.....ido na zaro na kalli marka'den sannan na kalle ta...." ta6'di Nanne marka'den wainar kika zubar?"
Sai tace dani " ai tunt6e nayi ban kula ba".
" To ki 'dauko robar mutafi gida...."
Hannu ta kai ta dago robar sai muka ga ashe itama ta face yayin da marfin ta yake nan garau jefe a gefe guda.

" ko zamu 'dan kwasa ka'dan?"
Nanne ta fa'da tana kallona" Sai nace kamamin mu sau'ke to sai in tayaki".

" ka'dan muka kwasa muka bari dan gaba d'aya ya lalace a wurin ba zai 'kara amfani ba.

Koda muka je gida kuwa Ummah bata ce komai ba jin cewa Nanne ce ta zubar kawai sai ta kar6i wanda muka kwasa 'din ta ha'da da ruwa da dama ta baiwa ragunan Baban mu suka shanye abinsu.....wannan dalilin ne ya sanya washegari bata yi waina ba harma da kunun baki d'aya.....sanadin kallon Deen da Nanne keyi wanda a lkacin ita kanta ma bazata iya shaidar ya san da zaman ta a duniya ba ko a'a duk da kuwa ha'duwar su da shi ta biyu kenan inda yau.
 



*****
      Tsananin yanda Deen ya saka Nanne cikin zuciyar sa ya sanya kafin sati har ya nemi duk wasu bayanan da ya kamata ya sani game da ita, cikakken sunan ta da sunan mahaifin ta harma da gidan su duk ya sani amma bai ta6a zuwa ba.

Da yake da wayo yake yin tambayar ba a fili yake fitowa ya bayyana manufar sa ba...misali ranar da zai fara yin tambayar aranar wani friend 'din sa yazo wurin sa ne sai da ya daidaici 'karfe biyu tayi sai ya jashi suka fito wajen gida suka zauna kamar da gaske, daka yanzun 'karfi da yaji yake tilastawa kansa zaman waje kawai dan ya ganta yaji sanyi cikin ransa..wani sa'in ma idan ya fito sallar azahar baya ta6a komawa gida koda kuwa 'karfe nawa zai kai a wurin to bazai ta6a shigewa ba sai yaga giftawar ta...(ni kuwa nace...aiki ya kama gwari).

NOORUL✔️Donde viven las historias. Descúbrelo ahora