P58

499 35 4
                                    

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*
 

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

_*Daga marubuciyar Littafin CAPTAIN ABBAS*_

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *58*

Mu kam muna ta murna da farin cikin ganin juna ni da su Saif ko fita bamuyi ba, Saif sun girma sun 'kara tsayi da fa'di kamar basu ba...ganin yanda nake 'ko'karin sakan jiki da sune ya sanya Ammi ta 'kira ni ta ja min kunne sosai akan.hakan...tace tsakani na dasu maganar baki ce kawai bata so taga ko hannu mun ha'da dasu saboda Allah ya haramta hakan tsakanin mu a yanzu tunda mun girma.

Hakan kuwa akayi dan ko da wasa ban ta6a kuskuren tsallake maganar Ammi ba ina kulawa da komai tsakanina da su Saif...balle Zaid kam ma dama sama-sama muke da shi har yanzu.

Duk mu da muke cikin gidan bamu ji labarin komai ba, gara nima ranar naji ana gulma akan Ma'un amma da Ammi ta kwa6e ni kan zancen shikenan ban kuma tada maganar ba haka kuma ban sa aka ba.

Anty Zainab ma muna yawan gaisawa da ita, da yake ma already ta koma Taraba so sai a waya muke ha'duwa kawai.

Kwatsam ranar sai ga waya daga mahaifi na da wata safiya, inda yake ro'kon Alhaji Baba da ya bari akai Hudah (ni) 'dakin mijina, bai fito fili ya fa'di dalilin sa na yanke wannan hukuncin ba amma duk da haka Alhaji Baba ya fahimci dalilin da ya sa shi fa'dar hakan cuz dama yasan lamarin ba zai ta6a 6oyuwa ba.

Cikin kwantar da murya yace da Baban mu
" Wai da ni cewa nayi idan yazo kawai ya sakam min ita tunda dama can bai san da maganar auren ba kaga shikenan...."
Taran sa Baban mu yayi da fa'din" A a Alhaji kar ayi haka, abashi matar sa kawai rabuwar ai bata da wani amfani".

Alhaji Baba zai sake magana sai Baban mu yayi saurin fa'din" Dan Allah Alhaji kar kace komai...kawai ni dai na ce abashi matar sa".

Dole tasa Alhaji Baba yin shiru ganin cewa mutun dattijo irin Baban mu ke ro'kon sa akan 'dan wannan lamarin yasan abin ya girmama ne...duk da yasan kawai dauriya ce yayi har ya sa shi iya yanke hukuncin akai ni 'dakin mijina alhalin yasan 6oyayyar halayyar mijin nawa.

Sai da ya zauna yayi nazari sosai akan hakan kafin for the first time tun bayyanar cikin Ma'u sai yau ya sami Ammi da maganar inda yayi mata bayani filla-filla harda abinda mahaifina ya fa'di.

Ammi kam shiru tayi saboda tsabar mamaki, wai jin Mu'een 'din ta ke da wannan alhakin, sai dai bata jin zata iya barin 'yar ta zama tare da shi, tunda rayuwar da ya zabarwa kansa kenan sai yaje yayi tayi...ita bata san me zata ce da shi ba.

Da yake ita ba shiga cikin jama'a take sosai ba dama da Ummah ta suka fi zumunci a kaf 'din garin , Ummah ta kuwa nasan koma menene zai faru bazata ta6a bu'dan baki tayi mata bayani ba...musamman ma da yake abin ya shafi 'dan ta ne na cikin ta.


Ammi kam bata 6oyewa Alhaji Baba ba take ta bu'di bakivta bayyana masa cewa ita bazata ta6a yarinyar ta zama da shi ba tunda haka halin sa yake...wannan abin.kunya da me yayi kama, mutun haka kawai batare da an tambaya ko matsa shi bavya 'dau ki kyauyar yarinya sukutum ya basu auren ta amma sai gashi tun ba'aje ko'ina ba sakayyar da zai musu kenan...hawaye Ammi take tsiyayar wa tsabar takaicin halin Yah Deen...cikinvranta take tuno ranar da ya ta shirga mata 'karya akan case 'din sa da Alhaji Baba akan Husnah ashe ninke ta yayi abai-bai har ta yarda shi cewa ba komai ke tsakanin sa da ita ba...ga shicda Allah ya tashi kama shi sai yasa shi aikatawa a inda bai isa ya musanta ko 6oye abinda ya faru ba...tace wallahi yarinya ta tafi 'karfinvta zauna da mazinaci yake can ya nemi irin sa amma ba 'yata ba.

NOORUL✔️Donde viven las historias. Descúbrelo ahora