P29

392 36 11
                                    

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*

 

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *29*

Cikin muryar kuka Hafsat tace " wallahi jinayi tamkar yanzu ne abin ya faru....ha'ki'ka mutuwa aya ce....Allah yaji 'kan Nanne..Allah haskaka 'kabarin ta...Allah ubangijin ka kyautata namu 'karshen"

" Amin yah rabbal Alameen".....Nuree tace gami da juyawa ta kallo 6angaren da Jas ke kwance.......Sannan a hankali ta cigaba da fa'din.
" Allah sarki Rayuwa....ban ta6a sanin na sha'ku da Nannen mu ba har sai da na daina ganin ta, zazza6i me zafi ne ya kamani.....ga sunbatun sunan Nanne da ya kasa barin baki na....ban kuma fasa kuka ba.

     Har akayi sati uku da rasuwar Nanne ban samu natsuwa ba, na kan yawaita tambayar Ummahn mu cewa " dagaske Ummah bazan kara ganin Nannen mu ba?....babu ranar da bana yin irin wannan tambayar tamkar kullum ba amsa iri daya ake bani ba amma gani nakeyi kamar watarana maganar bakin su zata canza...acemin zata dawo.

Nafi jin kewar ta idan na saka abinci a gaba na domin ada tare muke cin abinci ni da ita....muyi fa'da muyi da'di.

*****
Akwai watarana bayan rasuwar Nanne da kusan sati shida.... dan har an fara mantawa ma da rasuwar, tuntuni gida yayi shiru mun koma rayuwa mu ukun mu, Baban mu sai ni sai Ummah ta, to shi Baban mu ba yini yake agida ba sai yamma yake dawowa wataran ma har sai anyi maghrib, ni da Ummah ta ka'dai muke yini tare.....haka kuma tun rasuwar Nanne Ummah bata 'kara yin sana'a ba har yau....bama ta da niyyar 'karayi.

Lokacin da hantsi ne ina zaune 'kar'kashin bishiyar mango da ke cikin tsakiyar gidan mu.... Ummah ta naga ta fito daga cikin 'daki hannun ta ri'ke da wasu kayan sawan Nannen mu.

Kamar da gaske nace da ita " Umnah ina za'a kai kayan?"
Sai tace zan bayar ne Hudah babu amfanin ajiyar su ai ko?"
Tayi maganar tana 'ko'karin cusawa a leda.

Kuka kawai na sanya gami da tasowa na iso inda take....ina kuka ina fa'din " Ina zata kai min kayan Nanne, nace ta ajiye mata abin ta...in ta kyautar to in Nannen ta dawo ita me zata saka?".

Kuka nakeyi sosai wanda sai da na saka Ummah ma kuka, 'daki ta kona ta barni da kayan a waje na tattarasu gabana ina kukan da ambatan Nanne.

Ummah bata ta6a barmin koda 'dan kwalin bane da sunan inyi amfani dashi dan gudun rigima ta amma duk da haka bata tsira ba.

  Sallamar Ammi naji a tsakar kaina ban kula ba sai na cigaba da rera kukana " Subhanallah me kuma ya faru?"
Ammi tace tare da hanzarin isowa inda nake.

Bu'dan baki na sai nace " Nanne"
Salati Ammi ta sanya gami da tallafo ni haba " Hudah wmhar sai yaushe zaki bar wannan abin dan Allah?"
Ban kulata ba inata kukana sai ta sake fa'din " bakowa a gidan ne"
?"

Ummah dake tsaye daga cikin 'daki ne ta fito ta faman kakkauda kanta, tayi 'ko'karin tsaida kukan ta ne tun sanda taji shigowar Ammi, amma duk da haka kallo 'daya zakayi mata ka fahimci cewa tayi kuka.

Tabarma ta 'dauko ta shimfi'da wa Ammi sannan a hankali tace " barka da zuwa".

Kallon ta Ammi  tayi gami da fa'din " yauwa".

Bata 'kara ce da Ummah ta komai ba kawai ta dawo da hankalin ta gareni.

" Saurare ni please".
Tace dani....gami da gyara min zamana...." kalli nan"
Ta fa'da bayan ta nuna Ummah " waye wannan?"
Ta ce da ni tana kallon idanuna...cikin kuka nace " Ummah ta"
Banji ba ni share hawayen ki tsaida kuka ki fa'da da kyau inji.

NOORUL✔️Donde viven las historias. Descúbrelo ahora