P26

465 33 1
                                    

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*

 

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *26*

Hannu na ta kama da alamar rarrashi take fa'din " sorry daina kukan i ll slap him too...zan rama miki marin ki bar ni da shi kinji?"

Kaina na 'daga sama alamar " to" sai ta sake fa'din " yauwa Hudah ta...."

Juyawa nayi na kama hanyar barin kitchen 'din da fa'din " zan je in yi shirin makaranta Ammi".

" To adawo lafiya" tace min gami da juyawa ta cigaba da aikin ta.

       Ranar ma ko gaida Alhaji Baba ban tuna nayi ba kawai na nufi hanyar da zata sada ni da barin parlourn batare da na sake kallon koda  inda suke ba daga shi har Zaid 'din gaba 'daya.

Bayan fitata ne Ammi ta zo ta 'karasa shishshirya musu abincin, inda anan take yiwa Mu'een da har a lokacin yake kishingi'de a wurin fa'dan mari na da yayi.

Murmushi yayi mata kana batare da damuwar komai ba yace mata" wai dan Allah Ammi ina kika samo wannan yarinyar da sassafe haka?"
" Ina ruwan ka".
Ammi tace da shi  sannan ta sake fa'din " ni dai kar ka kuskura ka sake dukan min 'ya bana so"!...sassafe yarinya bata karya da komai ba sai ta karya da mari....idan kai aka yiwa hakan zaka ji da'di ne?....shiyasa nake son 'yan biyu na wallahi cuz duk iya wasan da zasuyi agidan nan bazaka ta6a jin sunyi duka ba......"

      Rausayar da kansa yayi gefe ganin da gaske Ammi ke masifar an ta6a yarinyar da be san ta bai kuma san me take yi agidan da wannan safiyar ba.

         Taran masifar tata yayi da fa'din " kai Ammi na sorry...ni dai abani abinci inci....yunwa nake ji".
Ya 'karashe da yamutsa fuskar sa.

" Je yiwa Alhaji magana to...".
Cewar Ammi

Sai yace " na shiga gaida shi ma na tarar baya nan...ina ya tafi da wannan safiyar haka?".
Ya 'karashe mahanar tasa da tambaya.

       
           Kai Ammi ta dafe gami da fa'din " ups na manta ai, yaje wurin ta'aziya ne amma bazai da'de ba zai dawo".

Bai damu ba sai ma yasake fa'din
" Ni dai abani breakfast please Ammi"!

Murmushi Ammi tayi tare da jan kujera tana shirin zama tace da shi......" sai yarana sunzo tukunna"

       Mu'een sai ya 'dan ha'de fuska gami da fa'din " haba Ammi...ni 'din bare ne ba 'danki ba?, Allah zanyi fushi fa....".
" Zama ka sa'k'ko ai..."
Tace tare da juyawa ta kallo 6angaren da Zaid yake zaune  daga can tsakiyar parlour tace da shi....." Zaid 'kira 'dan uwan ka kuzo kuyi break.... time is running".

Mintina uku basu cika ba sai gasu sun fito atare, Saif already har yayi shirin sa yayin da Zaid bai shirya ba har yanzun.

     Da kallo Mu'een ya bisu dukkan su inda ya sau'ke idanun sa kan Zaid dake shirin zama yace da shi " me yasa baka yi shiri ba kai har yanzu".

Kallon sa Zaid yayi sannan ya bashi amsa da fa'din " Assignment nake yi ne Yayah shiyasa".
" Assignment kake yi ko kuma wasan banza, ba kaine na ganka kuna guje-guje ba 'dazun?"
Zaid cewa yayi
" Takkadda ta ta 'dauka min fa shine nabita in kar6a ba guje-guje muke yi ba".
'Dan neman sai ya sake fa'din
" me yasa kuma sai yanzu zakayi Assignment 'din...tun jiya me kake yi?"
"Mantawa nayi sai yau da asuba na tuna".

NOORUL✔️Donde viven las historias. Descúbrelo ahora