P56

335 29 2
                                    

💕 *NOORUL* 💕
      (Haske nah)

By
*Salmerh MD*
 

*Wattpad @*
*Serlmerh-md*

💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASSOCIATION*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*

_*Daga marubuciyar Littafin CAPTAIN ABBAS*_

*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*

🅿 *56*

'Bangaren Yah Deen kuwa sam bai wani damu ba...ya riga ya 'kudura cikin ransa cewa zai dawo da Husnah cikin rayuwar sa kuma sai hakan ya faru no matter what.

Haka suka cigaba da rayuwa bai sake 'kiran layin ta ba kuma ko cikin school ma ba kullum suke ha'duwa ba saboda 6angare daban-daban suke..duk kuwa ranar da ha'duwar su ta kasance yakan bi tane da idanu kawai fuskar sa 'dauke da yalwataccen murmushi, musamman idan yaga irin shigar da tayi...cuz yanzu Husnah babban mayafi take sawa harda safa a'kafafun ta, wanda duk hakan ya kasance ne cikin dokar da Hisham ya gindaya mata, sai kuma akayi sa'a itama shigar ta kwanta mata sosai take jin da'din sa dan haka kuwa ba tare da damuwar komai take 'ko'karin bin umarnin sa duk da basa tare.

Bata ta6a tunanin komawa rayuwa da Mu'een ba tunda tayi aure...har wasu lokutan ma da kanta take ganin tsabar wautar da ta tafka abaya na biye masa suka ta aikata son ransu.

A kullum soyayyar sa na ma'kale da zuciyar ta amma tayi 'ko'kari sosai wajen ganin ta danne hakan, shiyasa ma ko sun ha'du cikin school bata yi masa kallo sau biyu, sau tari ma ta kan ga kamar ha'duwar tasu shiryayya ce kawai dan ya ringa bayyanar da kansa gare ta a lokutan da bata zato saboda kawai ya ringa tunatar da ita wanzuwar sa cewa still yana nan karta manta.

Ko 6angaren shi Mu'een 'din ma kuwa bai ta6a gigin sanar da su Ishaq cewa yana so ya dawo da Husnah cikin  rayuwar sa ba, ya bar hakan ne kawai cikin ransa dan gudun mitar Ishaq kuma yasan matu'kar Ishaq yasan hakan birki zai taka masa...ba zai barshi ba.

A kullum tunanin sa bai wuce taya zai sake mallakar ta ba..duk wani hanya da yayi tunanin zai 6ulle masa sai kuma yaga abin ba haka ba saboda Husnah duk ta canza yanzu kamar ba ita ba...kwata-kwata ta 'dauke masa wuta, bai ta6a tunanin Husnah zata iya yi guje masa cikin lokaci 'kan'kani haka ba...shiyasa sau da dama ya kan tsinci kansa dumu-dumu da jin haushin mijin da ke auren ta a yanzu dan yasan shine sanadin rabuwar su....(ni kwa nace ka manta Addu'ahr da ka ringa yi abaya kenan?)

Kwatsam ranar yana gida dawowar sa kenan daga lecture sai yaji 'karan wayar sa, ko da ya 'daga sai yaga sunan Ishaq na yawo kan fuskar wayar, batare da damuwar komai ba ya 'daga nan Ishaq ke tambayar sa wai ko yana gida ya bashi amsa da" erh yana nan".
A takaice.

" Gamu nan zuwa to yanzu".
Fa'din Ishaq daga 'daya 6angaren.
Mu'een sai yace
" Kun fasa fitan ne kuma?"
" Ah no bamu fasa ba... ai ba zama zanyi ba yanzu zan koma".
" Ok sai kazo to".

Da haka suka yi sallama kowa ya ajiye wayar sannan ya ci gaba da abinda yake yi ba tare ya ko yi tunanin me ze kawo Ishaq wurin sa a dai-dai wannan lokacin ba tunda yasan basu da'de da rabuwa ba kuma kafin rabuwar su bai sanar da shi cewa zai zo ba.

Yana zaune a wurin yaji sallamar Ishaq daga bakin parlourn sa sai ya amsa a hankali tamkar bai son yin magana kamar yadda ya saba yin komin sa cikin ra'ayi.

Ishaq ne ya fara shigowa kamar daga sama sai ga Husnah a bayan sa ta sha Hijabin ta ash colour wanda yake babba har 'kasa ya kuwa yi mata kyau ta fito shar abinta gwanin birgewa.

Kallo 'daya tayi masa ta 'dauke idanun ta daga kansa...kishingi'de yake har yanzun bai motsa ba sai ma yayi kamar ganin su taren bai sa yaji wani abu makamancin mamaki ba.

NOORUL✔️Hikayelerin yaşadığı yer. Şimdi keşfedin