💕 *BINTEE*💕
*( 'Yata ce)*Wattpad@
Serlmerh-md🅿️ *...34*
.......Satin Adam biyu a asbiti kafin aka sallamo shi, duk ya rame ya zam tamkar ba shi ba, abu 'daya kadaivne bai canza game da shi ba shine gayun sa, shima 'din ba kamar baya ba dan a har yanzun ba cikin natsuwa yake jin kansa sosai ba.
Duk yadda Hafeez da Hajiyar sa suka so ya kara samun nutsuwa ki yayi, Hajiya da kanta tai masa alkawarin nema masa Zaitun ita dai burin ta ya samu natsuwa amma ya kiya.
Adam yasha bakar wahala wajen neman Zaitun amma sam ya gaza cimma burin sa, bai kuma ji ko da wanda ya ganta bane balle lbrn inda suke...sai da Adam ya koma tamkar mahaukaci sbd neman Zaitun amma ya rasa ta, gefe guda ga damuwar abinda mahaifin sa ya aikata ya kasa barin zuciyar sa.
Daga baya ya nemi gidan mahaifiyar Dr Rashed da tunanin ko tana tare dasu amma suka ce basa tare da ita, sun nemi ta biyo su amma taki amincewa hkn kuma basu san ina take ba a halin yanzu.
Da 'kyar Adam ya saduda ganin kamar Zaitun tayi masa nisan zango ne nisan da baya jin zai iya samo ta anan kusa..dole badan yaso ba ya hakura amma bai cire rai da samun ta ba watarana.
Sai da aka sake shafe wasu kwanaki kafin da ban baki Hafeez ya sa shi agaba suka kaiwa Alhaji Jibrin ziyara a prison, a hakan ma da 'kyar aka barsu ganin sa, dan killace yake a wuri na musamman.
Hakika 'dan Adam ba'a bakin komai yake ba, idan kaga yadda 'Dan Maliki duk yayi sanyi bazaka ta6a 'dauka wannan mutumi mai izan nan bane, bazaka zaci cewa wannan mai tunkaho da dukia da karfin mulkin siyasan nan bane wanda jama'a ke matukar martabawa...rayuwa kenan.
" Al..ha...ji"!
Adam ya furta sunan sa a mamakance gami da mi'kewa tsaye ganin cikin 'yan kalilan din satikai gaba 'daya kamanin sa sun sauya zuwa wani daban, zama yayi bisa kujerar da ya mike yana jin idanuwan sa na tara ruwa...Innalillahi wa inna ilaihiraji'un...
Ya furta a fili 'kasa 'kasa yana jin wani abu mai kama da tashin hankali yana shigan sa.Shi har 'Dan Malikin da ya zaune kujerar dake zaune facing da Adam 'din kasantuwar baya iya jure doguwar tsayuwa a yanzu jiri ke 'diban sa, dukkan su kwalla suke zubdawa, babu wanda ya iya furta komai daga cikin su
Abu guda da yafi damun 'Dan Maliki ya kuma fi tsaye masa a zuciya bakomai bane face tunanin yadda Adam zai kar6i maganar, dama tun ma kafin faruwar lamarin ya riga yayi nadamar komai ya kuma zanta da Hafeez ya sanar masa duk niyyar sa, sai dai bai san ta yadda 'adn nasa zai kar6i zancen bane, tuni kuma ya fara neman gafarar ubangijin sa yana.fatan kuma ya yafe masa duk kuraransa kafin.lokaci ya 'kure masa.
Yasan kuma.wannan duk shirin ubangiji ne, ya riga ya tsara masa sai ya kar6i wani hukunci tun anan dunia kafin haduwar su aganin sa shiyasa har maganar ma ta bayyana bai kuma yi bakin ciki sosai da hakan ba, a iya sanin sa abinda ya shuka ne zai girba amma tunanin sa Adam ne, musamman da yasan cewa yana da ciwo sanadin damuwar sa sai ga wannan kuma...wani hali zai shiga, ya zaiji idan wannan labari ya riske shi...kullun tunanin sa kenan.
A yau kuma da Adam ke zaune gaban sa banda tsananin kunyar sa babu abinda yake masa kai kawo, sosai yake jin babu dadi idan ya tuna makomar da Adam din zai iya fadawa, sai gashi ayau 'din daya gansa ma duban farko ya fahimci Adam din ba karamar wahala yasha ba duba da yadda duk ya rame ya zam sai 'kashi duk wata kumari tasa babu ita...wai sai yaushe ne zai daina azabtar da zuciyar bawan Allahn nan.
'Bangaren Adam kuwa rasa ta inda zai fara ma yayi, bai san me ze ce da mahaifin nasa ba, shin jaje zai masa ko kuma gaisuwa game da faruwar lamarin?, bazai iya ko guda daga ciki ba, gaba 'daya ji yayi komai ya kwance masa, wata zazzafar 'kauna da tausayin mahaifin nasa suka diram masa lokaci guda fin ma kaunar da yake yi masa abaya, meyasa ya za6i wannan hanyar wajen tara dukiyar sa..?
Meyasa bai yi tunanin makomar da hakan zai iya jefa shi ba da duk masoyan sa...?
Sosai yake zubda 'kwalla kansa a kasa, ya ma kasa duban 'Dan Maliki sau biyu tun duban farko da yayi masa bai iya ya 'kara ba, gashi wannan karon Hafeez bai biyo shi sun shigo ciki ba cewa yayi zai jira shi awaje balle ya 'kara masa 'kwarin gwiwa.

ESTÁS LEYENDO
BINTEEE ( 'Yata ce)
Ficción GeneralSome people succeed because they ar destined to, but most people succeed because they ar determined to....