BABI NA 27

604 67 6
                                        

*🏌🏼‍♀ISMAHA ZAINAB 💍*

©BY *😘Um Nass 🏇*

® *NAGARTA WRITER'S ASSOCIATION*

_Alhmdlh! Munyi biki lafiya mun kuma gamashi lafiya. Na gode da Addu'ar fatan alkhairin dana samu abakunan ku._

Babi na Ashirin da Bakwai (page 27)

Kwantar da Hussain tayi, ganin yayi barci tuni, sanan ta tofesu da Addu'a dukansu su biyu.
Ko wani motsin da take akan idon Alh. Isah yake, aransa yana girmama nutsuwa irin ta Ruqayya "Komi naki mai kyau ne Ruqayyah." Ya faɗa yana murmushi gami da kafeta da idanuwansa.

Ido ta lumshe ta buɗe su tarr akan nasa idon, sanan ta mayar masa da salon murmushin sa "Duk abin da kaga yayi kyau a duniya ta na tabbatar kai ne silar faruwar sa Abu Usama."
Kai ya girgiza ba wanan ne karo na farko da yayi yabo agare ta ba, ta dawo da yabon kansa, wanan yana cikin hikimar iya sarrafa harshe irin na Ruqayya, take kuma kwashe rabo mai yawa na muntutakar da yake yima sauran mutane.

"Har yanzu babu abin da ya sauya agareki. Lokuta masu yawa nakan ɓata lokaci wajan nazari da ganin wauta irin na mijin da yayi sake kika kuskure masa."
Mikin da yake zuciyar ta ya tada mata, kewar da tayi na gida da iyayen ta duk sun dawo, hawaye ke barazana sauqa akan idon ta tayi saurin riƙeshi, kana ta fuskance shi "Akwai ƙaddara wadda take rubuce acikin littafinmu, wasu lokutan mu ci karo da mai zaƙi, ayayin da kuma wata take tafiya da mugunyar ɗaci mai ɗatata zuciya da maƙoshi. Idan kuma ka saita fuskar ka ga kallon su Hussain zaka fahimci ƙaddarar data fitar da su atsakanin mu ita ce ta zama mafarin barin mahaifa tah!" Ba zaka ɗauka akwai damuwa ashimfiɗe akan fuskar ta ba, ayayin da take fidda ko wata kalma ta maganar ta ba. Amma kuma a baɗini ranta kamar wuta take jinsa, ga faɗuwar da gaban ta yake har yanzu ƙara ƙaruwa take.
Miƙewa tayi ta da sauri "Bari nayi alwala Abu Usama, wani abu na shirin faruwa da ni, wanda da alama ba na alkhairi bane."
Da ido ya bita har ta fice aɗakin, maganar ta akwai maƙurar gaskiya wanda babu son kai da son zuciya acikin ta, idan kuma yayi nazari ya fuskanci idan ta nufa kamar tana masa tuni akan ba dabara ko wauta ke sa mutane samu da rasa abin da yake mallakinsu ba, wani aciki ikon Allah ne.
Bai ji motsin shigowar ta ba sai gani yayi ya fara sallaha, hakan ya sashi miƙewa ya nufi nasa ɗakin dan ya samu fuskantar wasu abubuwan da ke gaban sa.

Ta daɗe tana Addu'a hawaye na zuba akan idanuwan ta, mafiya yawan Addu'ar tata akan Ismaha Zainab ne na nema mata kariya daga mugun abin da zai same ta aduk inda ya ke.

********
Ƙafarta ta fara jefa wa cike da gushewar hankali, ko ina ajikinta rawa yake da karkawa, amma abun mamaki babu wanda ya kula da jirkitawar kamanin ta, asalima hankalin su yayi gaba wajan kuka da fifita ƙafafuwansu.
Inda ta hango taron firifawa ta nufa kamar ana hankaɗa ta saboda saurin da take, taku uku ya rage ta ƙasa kusa da su, kamar ƙiftawar ido wani farin haske ya shige jikinta, tsayawa tayi cak kamar an dasata awajan, ahankali kuma numfashinta ya fara sassarƙewa nan ta tsugunna awajan tana dafe da ƙirjinta.

Tahowa firifawan suka yi sai a lokacin suka ankara da wanzuwar su awajan "Kee!" Siniyo Laure ta faɗa kasancewar ita ce tafi kusa da ita.
Bata ɗago ba balle suyi tsamanin ta jisu "Kan ubaccan." ta faɗa tana ƙoƙarin sauƙe bulala ajikin ta.
Ɗagowa tayi da idanuwan ta da suke gama hargitsewa saboda azabar da take ji aran ta, gefe ɗaya kuma ta kasa sarrafa kanta, wani abu ke shamaki da barazana da lafiyar ta, tana so ta ƙarasa tana ji an riƙe ko wata jijiyar da take jikinta.
"Uban mi kika tsaya yi anan? Kinaga sauran ɗalibai ba kowa sai ke tabbacacciya shahararriya ko?" Siniyo Jummai ta faɗa tana fiffito da idanuwan tah, ganin yanda Laure ta tsaya awaje ɗaya.
"Ina-ga-fa bata da lafiya." Siniyo Shamsiyya ta faɗa tana ƙoƙarin ƙarasawa kusa da ita da fuskar tausayi.

Kafin ta ƙarasa kuma Jummai ta tare ta "Wasu lokutan ke kike siyo mana raini awajan jiniyas ɗinmu, taya kinaga yarinya fess da ita amma kice wani bata da lafiya? Tantama nake akan alaƙar da ke tsakaninki da ita. Mi kika ɗauke ta? Mi kuma kika ɗauke mu?"

Tsayawa Siniyo Shamsiyya tayi cak, juyowa tayi tana kallon Jummai da sauran firifet ɗin da suka tsaya suma suna kallon ta da alama jiran amsar da zata fito abakinta "Kamar ya? Wata banzar magana kike Jummai?"

"Uhm! Kinfi kowa sanin abin da nake nufi, ko wata rana kulawar ki akan yarinyar nan tana yawa, idan bata da lafiya mi zai tsayar ta anan? Kina ga idon ta fess akan mu."

Magana take son yi amma kuma ta rasa abun da zata faɗa mata saboda ta kaici, ji tayi an dafa kafaɗar ta wanda yasa ta juyowa, Lateepha ce tana mata murmushin da bai kai zuci ba "Idan kina son ta ba sai kinyi haka ba, xaki nunawa duniya matsayin da take da shi awajan ki ba. Ki saurari zuciyar ki sai ki tsaya akan ƙafafuwanki. Na tabbata ayanzu bakya buƙatarmu kamar yanda kike buƙatar kasancewa da ita."
Tana gama faɗar haka ta wuce ta barta anan tana yima su Jummai magana akan su tafi lokaci na ƙurewa, da ido ta bisu da kallo tana girgiza kai _"Adai rayuwa irin ta makarantar kwana, ko yaya ka aikata kulawa da tattalin wanda ƴake ƙasanka sai an maka bahaguwar fassara"_
Ƙafafuwanta ta ja ta ƙarasa kusa da Ismaha Zainab wanda take tsugunne tana kuma riƙe da ƙirjinta. "Bismillahi" ta faɗa tana riƙo hannun Ismuha Zainab, akan neman tsarin Allah daga sheɗan wanda yake son rinjayar zuciyar ta zuwa mummunan alaƙar da take fatan shimfiɗawa tsakanin ta da yarinyar.
Kamar an jona mata shokin ɗin wuta haka Ismaha Zainab taji, cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kuma nutsuwar ta ta dawo jikin ta, nauyin da take ji a ƙirjin ta ya ɗauke cak, baki ta wangale tana dariya ganin wanda ke kusa da Ita "Anty Mai Kyau." ta faɗa cikin muryarta mai cike da karaɗi.

"Mi kike anan ke ɗaƴa?" ta jefa mata tambaya tana ɗaga mata kai.
Juye-juye ta fara yi amma ganin babu kowa ya sata saurin tashi tana kakkaɗai jikin ta "Tare muke da su Maryam fa anan."
Kallon ta tayi, ta lura da yanda ta ruɗe a lokaci ɗaya "Tashi mu tafi kawai, kinga babu kowa anan."
Tashi tayi ba tare da tace komi ba, suka nufi wajan Assambili kasancewar litinin ce, sauran ɗalibai duk sun hau layi baka jin motsin kowa, saboda tsayuwar firifet atsakan-kanin ko wani layi da yake wajan.
Sata tayi alayinsu tana murmushi ta shafa kanta "Ki daina bari ƴan ajin ku na ɓace miki."
Kai ta gyaɗa mata ba tare da tace komi ba, sai murmushin da take mayar mata da shi itama.

*********
Bayan mako biyu.

Alokacin ne aka gabatar da hutun ɗalibai bayan kammaluwar jarabar zangon karatu na farko.
Ismuha Zainab ta zo amatsayin ɗaliba ta biyar, acikin su 96 ɗin da suke ajin, ihun kuka take wai malamin ya cuceta duk ita take na ƙawayen ta jarabbawa amma kuma sun fita da maki.
Takaici da haushi ya kama sa'adatu ta bige mata baki "Gobe ma sai ki ƙara basu ai, uwar kinibibin tsiya."
Tana gama faɗar haka ta tashi ta barta.

Dole ta ƙunshe vakinta tayi shuru, ahaka suka ci gaba da shirya kayan tafiyarsu hutu gida.

Ranar Juma'a:

Duka ɗaukacin ɗalibai na murna da Ihun tafiya gida, ayayin da Ismuha Zainab take jin kamar ta wuntsula dan murna.
Cikin sa'a sai ga Usama yazo ɗaukanta shi da wani abokinsa, ai da murna taje ta tare shi.
Ihu take tana maqaleshi wanda sai da ta kusa kadashi ƙasa "Dan Allah kiyi haquri ki sakar ni." kalmar da ya faɗa awahale, yana takaicin zuwan da yayi ɗaukanta, wanda Alh. Isah ya takura masa.
Sakin sa tayi sanan ta tuntsure da dariya "Kaga in-da ka zama tulele acikin wata ukun da nayi ban ganka ba?"
Kallon jikinsa yayi sanan ya girgiza kai "Ai dole, saboda babu ciwon kai agidan mu acikin wanan watannin."

"Ayya kace kun sha ciwon kai ban sani ba, amma dai ban da Luyya kai kaɗai kayi sa?"
"Ina kayan ki ne? Kizo mu tafi lokaci na ƙurewa, kin san yau Juma'a akwai xuwa masallaci agaba na."

Juyawa tayi da gudu tana faman rugawa Anty Sa'a kira, anan suka haɗu da Siniyo shamsiyya da Murna take faɗa mata anzo ɗaukan ta, sai an koma hutu kuma.
Kai ta shafa mata "Muje na ga tafiyarki to. Mu sai anjima"
"To" tace tana riƙe hannunta, anan suka haɗu da Sa'adatu har ta kai kayan su.
Har mota siniyo shamsiyya ta rakata, suka gaisa da Usama da yake ya faman washe mata baki, sai da taga shigarsu mota ta risina ta ce ma Ismaha Zainab "Ki gaida min da Luyya sosai."
"Za taji in sha Allah, nima idan kije ki gaida min da maman ku." tana yalwata Murmushi akan fuskar ta, ta maida mata da martanin Murmushin ta.
Dariya Siniyo Shamsiyya tayi sanan ta girgiza kai, yarinyar nan akwai surutu, har motar su ta fita a makarantar tana tsaye tana ɗaga musu hannu.

******
Haɗejia loading........

🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀
Vote da cmnts naku yayi qasa fa, da alamu labarin baya shigarku, bakwa buqatarsa kamar yanda ƴan whtspp ke sonsa. Zan jingine yin published nasa anan, dan naga akwai gajiya wajan karantawa fiye da rubutawa.

#NWA
#ISMUHA ZAINAB
#CMNTS, LIKE, SHARE
#UM NASS
#GIRMAMAWA

ISMUHA ZAINAB CompletedStories to obsess over. Discover now