BABI NA 17

473 45 1
                                        

*🏌🏼‍♀ISMAHA ZAINAB 💍*

©BY *😘Um Nassb🏇*

®NAGARTA WRI. ASSOCIATION

  _Allah sarkin daɗi inji ɓarawon takanɗa. Duk ta yanda naso na bayyana jin daɗina da godiya agareku abin ya girmi laɓɓana. Allah kaɗai ke iya gane karatun baibai alokacin daya faɗa duniyar masu kunne. Yanzu ne na qara miqe qafa na kuma girmama kalmar da kowa yake faɗa akan KIMA! Kuɗi zai iya siya maka komi amma banda ita, dan haka komi zaka rasa arayuwa ka rasa amma karka taɓa bari ka rasa kimarka._

*😃Mai Dambu ke ko! Acikin mutane masu dama da suke kewaye dani zance ke ɗaya ce tilo da kika zama daban acikinsu, ta fuskar magantu da kowata kalma da ta zama mallakin bakinki, ina miki fatan alkhairi ina kuma fatan zumuncinmu ya ɗore har gaba da Abadan, ngd sosai*
 

BABI NA SHA BAKWAI (Page 17)

  Cirko-cirko mutanen gidan sukayi kowa ya kasa ƙarasawa wajansu, Salamatu kam ɗaurin ƙirji ne ajikinta hakan yasata ƙin ƙarasawa dan bata manta abin data mataba. Kuma har ga Allah ita yarinyar tsoro take bata yanzu, ta ɓangaran Rabi ma ko kaɗan batayi gigin karɓar Usama daga ɗamarmareshin da Ismaha Zainab tayi ba, acikin zuciyarta daɗi take ji dan dama yafi kowa mugunta agidan da baƙin hali.

  Numfashi yake fuzgarwa, da ƙarfinsa yake ƙoƙarin rabata da jikinsa, amma kuma hakan ya gagara, ga ɗan banzan ihun kukan da takeyi wanda ya cika masa kunnuwa.
Tsawa Luyya ta kwatsa mata wanda bata taɓa yi mata irinta ba, dan yanzu abun na Ismaha Zainab ya zama rigima kuma, amma madadin ta tsorata ko ta sake shi, sai ta ƙara cuno baki tana maka mata harara, wanda tasa gaban Luyya faɗuwa, wannan ba Ismaha Zainab bace, ta faɗa acikin zuciyarta gaban ta naci gaba da faɗuwa.

hakan yasata yin shuru, sai dai ga Ismaha Zainab ƙara tunzura ta tayi ta ci gaba da maƙalƙaleshi "Allah bana co."

Ganin idon mutane gidan akansu yasata aro dauriya da juriya taci gaba da yi mata magana, amma azuciyarta tsoro ne fall ranta "Ki sake shi nace, ko kuma ranki ya ɓaci yanzu nan."

Kamar tana ƙara cewa ta ruƙun-ƙumeshi haka ta masa, shi kansa ya gaji, ya jikkata dan jin nauyinta yake kamar na ƙartai goma ne suka danneshi, hawaye yake akan fuskarsa da ƙyar ya haɗa kalmomin bakinsa ya fara mata magana "Kiyi haƙuri ƙanwata ki ɗaga ni, Allah daga yanzu bazan ƙara dukan kiba." ya faɗa cikin dashasshiyar muryarsa wanda take futa da ƙyar.

Hakan yasa yaran gidan Ihu da ilo, wanda Ismaha Zainab ta ƙara musu da ƙarfafa gwuiwa ta hanyar cewa "Ƙato Udama na kuka, maza sai ka min doki iya baba ko jan cauka" kafin ma ta ƙarasa maganar ya tsugunna akan ƙafafuwansa ya fara mata, bai kuma damu da cewar gidan akwai cukowar mutane acikinsaba, aransa yana takaici yana kuma jin ɗaci yanda yarinya ƙarama ta zame masa jidali.

Dukansa yaji tanayi tana halba ƙafafuwanta "to to baka waqal idan kana tafiya."

Cikin sauri ya fara "Doki iya baba, doki iya baba."

"BA haka akeba Allah ni na fasa sauƙa."

"Kiyi haquri ban iya ba, ki koya min kinji?" dariya tasa da ƙarfi Su Hafsat da khadija na tayata.
Takaici yasa su Salamatu komawa ɗaki duk da suma suna dariya, Usama ɗan ƙwalisa yaron da ko aikensa ba'ayi agida, yau gashi ya ƙare da rarrafe agidan, akuma gaban ƙannensa da ko inuwa ɗaya baya ƙaunar ace sun haɗa.

"Assha! Ya da haka kuma ƴar baba?" maganar Alh. Isah wanda shigowarsa gida ya tsinkayi sabon aikin da ake, dan yau futar wuri yayi kasuwa kasancewarta lahdi, yana da baƙi masu sari.

Sauƙa Ismaha Zainab tayi daga bayan Usama taka kakkaɗe hannunsa "Doki Iya baba ya min." ta ƙarasa tana washe bakinta.

Kallon Usama yayi, wanda ya gagara tashi zaune fuskar nan kamar an aiko masa da saqon mutuwa "Da girmanka kake wasan rarrafe atsakar gida. Ko kayan arziqi babu ajikinka."

ISMUHA ZAINAB CompletedStories to obsess over. Discover now