34

605 64 0
                                        

*🏌🏼‍♀ISMAHA ZAINAB 💍*

©by *😘Um Nass 🏇*

_Follow me on Wattpad @UmNass_

Page 34

Murmushi yayi bayan ya gama sauraran abin da Aljanin Ismaha Zainab ya faɗa, ba tare daya yi magana ba ya fara karatun ruƙiyya, nan ta fara ihu da murgine-murgine, sautin kuka kala-kala wanda yasa Luyya tsorata ga wani tausayin Ismaha Zainab daya kamata, ganin yanda ta fara bubbuga kanta aƙasa.
Miƙewa tsaye Musaddiƙ yayi yana buɗe Muryar sa da sauri-sauri yake karatun hakan yasa Ismaha Zainab dunƙulewa awaje ɗaya, kukanma ya gagara sai matse kanta da take da hannun ta.
"Dan Allah kabar karatun nan kana ƙona mu, kayi haƙuri zamu fita yanzu." cikin wata wahalalliyar Murya wanda Amon ta yake fita da ƙarfi-ƙarfi akayi maganar.

Shuru yayi sanan ya zauna yana fuskantar Ismaha Zainab da take duƙunƙune wanda azahiri take nan, amma abaɗini mutanen kanta ke kusa.
Fuska ya tamke sosai cikin dakakkiyar muryar sa da take fita da ɗan ƙarfi, duk da sanyin ta amma jin sautinta kan iya sa buguwar zuciya "Mi yasa kuka shiga jikin ta? Tun yaushe ne kuke wahalar da ita haka? Aiko ku akayi ko kuma ku kuka aiko kanku?" tarin tambayar da ya musu wanda tasa Ismaha Zainab ɗagowa idanuwan ta har yanzu ahargitse suke gwanin tsoro, harara ta aika masa sanan ta mayar da kanta ba tare da tayi magana ba.
Kai ya gyaɗa sanan yaci gaba da karatu, nan tasa ihu da kururuwa "Nace kabar ƙona mu, kasan shekarun da nayi ina jikin ta? Kana ina nake bata kariya aduka tsawon shekarun ta? Haba ka tausaya min mana, ka min adalci akan ta." cikin murya mai wahala da sauti marar daɗi ake maganar.
  "Naga kamar kafi son na ƙona kan ai, wani adalci kake magana bayan wahalar da kake bata da iyayen ta."
"Ni ban taɓa bata wahala ba. Asalima kariya nake bata a iya tsawon rayuwar da mukayi tare, ko iyayen ta basu san da zamana atare da ita ba saboda kawar musu tunanin da nake yi, amma lokaci ɗaya daga zuwan ka komi nawa ya taɓarɓare, kasa abun da na fusata har na zo kowa ya gane."
Kallon-kallo ake tayi tsakanin Alh. Isah da Luyya suna mamakin maganar da Aljanin yake, a ina Malam ɗin ya san ta, asanin Alh. Isah da Luyya baƙo ne awajan su, kusan ma yau ya taɓa ganin sa.
Tunanin su ne ya katse lokacin da sukaji Muryar Musaddiƙ  na daka wa Aljanin tsawa "Ni ba wanan na tambaye ka ba, mi yasa ka shiga jikin ta? Abin da kawai na tambaye ka."
 
"Akwai wata rana da suka je gidan Innar kamalu, to alokacin Mamarta ta tafi tabarta agidan, bayan sun mata horon yunwa sun dake ta suka shanya ta arana, to alokacin ni kuma nazo wucewa kasancewar gidan hanya ta ce kuma akwai wani ɗan uwanmu awajan bolar gidan, duk abin da sukayi akan ido na wanan yasa naji tausayin yarinyar, musamman da naji Tani tana ƙoƙarin yi mata asiri saboda tafi yaran ta kyau."
"Hasbunallah wani imal wakil." kalmar da Luyya ta faɗa cikin karkarwar murya da tsoro, ta dafe ƙirjin ta da yake barazanar ɓallewa saboda bugawar da zuciyarta take yi.

"Daga lokacin sai na zama kullum ina tare da ita, nakan zo na jata muyi wasa awajen da ba kowa xai ganta ba, ahaka wata rana Innar Kamalu tazo da Tani suka fara yima Luyya masifa akan ta bar sana'ar ta, har suka fara jifa da kayan siyarwar tata, alokacin Tani tazo da ƙullin maganin da zata yima Ismaha Zainab asirin da babu wanda zai so ta, ƙarshe kuma ta shiga duniya da yawon karuwanci, to shine sai nazo asiffar Ismaha Zainab na zane su da bulala, sanadin da asirin ya karye baiyi tasiri akanta ba, to kuma a ƴan tsakan-kanin lokacin Idiris ya dawo daga tafiyar da yake, haka kuma su Tani da Innar kamalu suka tusashi da ƙaryace-ƙaryacen banza, bayan sun bashi ruwan da yake ɗauke da Asirin da xai tsani Luyya, aranar bana nan gaskiya ina ƙasar habasha na je duba kakana, koda na dawo rigimar sakin da yayi ma Luyya na tadda to shine na yanke kawai ta bar garin, na kuma ci gaba da hura mata wutar ƙiyayyar garin ta hanyar bin hanyar da babu wanda zaiyi tsammanin tana nan."
Tunda ya fara maganar jikin kowa yayi sanyi acikin su, musamman Musaddiƙ da ya cika da mamaki "Wacece Tani ɗin da Innar kamalu?" tambayar daya samu kansa da yima aljanin kenan, saboda girman lamarin da kuma abin da suka aikata ga Luyya.

ISMUHA ZAINAB CompletedWhere stories live. Discover now