BABI NA 14

427 52 0
                                    

*🏌🏼‍♀ISMAHA ZAINAB 💍*

©by *😘Um Nass 🏇*

®NAGARTA WRI. ASSOCIATION

Babi na sha Huɗu (page 14)

Ganin da tayi ta nufota da gudu yasa ta ruga ta ɓuya abayan Luyya, can kuma ta saketa tace "Luyya balni zakiyi ta dukani" sai ta ruga bayan Alh. Isah tana "Sabon Babu kalka bali ta duka ni, kaga dai tuleliya ce mutuwa zanyi idan ta dukani" haba nan suka ƙara tuntsurewa da dariya.

"Ai yau babu Uban daya isah ya hanani dukan wanan shegiyar yarinyar agidan nan, idanma abaya kinama mutane iskanci suka ƙyaleki toni yau baki isah ki minba" wawuro ice tayi atsakar gidan ta nufi inda Alh. Isah yake Nanfa Ismaha Zainab ta callara qara, tana ruƙunqlƙume Alh. Isah "Sabon Babu kalka bali ta dakeni, Allah ƙalfi zatayi kaga mulyalta irin ta ƙatun maxa ne."

  Saurin rufe bakin Ismaha Zainab yayi da ɗaya hannunsa, ɗaya hannun nasa kuma yana riqe da cikinsa, saboda dariyar da yake, cikinsa ya ƙulle, wai muryar maza ga Salamatu.
  Duka yaran gidan da mazan dariya suke idan aka ɗauke Salamatu da take jin ta muzanta, bata taɓa jin ɓacin rai irin na wanan ranar ba, afusace ta finciko Ismaha Zainab zata daketa, hakan yasa Luyya runtse idonta dan ko kaɗan bazata hana Salamatu dukantaba.

Aɓangaran Alh. Isah kuma ƙarfinsa ne ya ƙare wajan dariya, yayi maganama ya kasa dan har yanzu bai bar yin dariyarba, sai kallon Salamatu yake yana jin wata dariyar na zuwar masa, yasan dai ƙatuwace amma bai taɓa lura girmanta yakai akirata tuleliliyaba sai yanzu daya ganta agabansa ɗaure da zani kamar doyar da aka lilliɓama tamfal.
 
Gefe ɗaya kuma Rabi ce kishiyar Salamatu itama dan dariya har zama take gashi ko kari basuyiba suka tashi da wanan abun dariyar, suma yaran sai yi suke.
Itacen ta ɗaga zata daketa nan Ismaha Zainab ta cukuikuye zanin nata ta shige jikinta, kafin tayi yunƙurin cireta ajikinta kuma hannunta ya gaji ƙarshe icen ta ajiye ta fara ƙoƙarin ɓam-ɓareta ajikinta cikin rashin sa'a ta cireta ita da zanin jikinta daya yage saboda riƙon ƙarfin da Ismaha Zainab ta masa, saurin durƙushewa Salamatu tayi saboda babu komi ajikinta sai gajeran wando dabai kai gwuiwartaba, ina rami ta afka haka takeji awajan.

  Ba shiri Alh. Isah ya karɓe zanin daga hannun Ismaha Zainab da take ta dariya tana nuna Salamatu, sauran ƙananan yaran suma suna dariya "Lah kunga Maama da wandon maza" hawaye ne ya shiga zuba acikin idon Salamatu wanan tozarci har ina, bata taɓa jin kunya da takaici kamar na yauba, yarinyar cikinta itace ta mata wanan ɗanyan aikin? Kafin tayi wani yunƙuri taji an lulluɓa mata zani ajikinta Alh. Isah ne yana ƙunshe dariyarsa "Yarinya ce, bai kamata ki biye mataba, yanzu gashi agaban yara kinji kunya." tashi tayi ta xari buta ta shige makewayi.

_"Zan koyawa wanan Aljanar yarinyar hankali."_ kalmar data faɗa kenan tana ɗauro alwala, ko sallah batayiba wanan masifar da mi tayi kama.

  Aɓangaran Luyya kuma kai ta girgiza tana aikama da Ismaha Zainab Harara "Allah ya shirya min ke Zainab." sanan ta matsa kusa da Alh. Isah wanda har wanan lokacin bai bar murmusawa ba "Alhaji mi za'a dafa na karin safe? Ga yara sun tashi."

Kallonta yayi cike da murmushi akan fuskarsa, kana ya juya kallonsa ga yaran "Mi kuke son ci yanzu?"

Cikin haɗuwar baki sukace "Doya da ƙwai da biredi da shayi." kallonta yayi cikin murmushi sanan yace.
"To kinji abin da zaki dafa." yana gama faɗar haka ya shige ɗakinsa, wani takaici da haushi ne ya kamata "Ikon Allah ana tambayarka kana tambayar yaranka."
Komawa tayi tayi ɗakinta ta ɗauko tukunya ta haɗa ice kana ta nufi ɗakin Salamatu "Yaya ina kayan abincin suke?"
Harara ta aika mata saboda har ga Allah haushinta takeji musamman yanzu da sukayi rigima da ɗiyarta "Jeki Rabi ta nuna miki." daga haka ta karkace ta kwanta ranta na mata suya, amma kuma Ruqayya ta cika mata ido ba zata iya mata rashin mutuncin data so yi mataba.

Bata ɓata lokaciba ta fara haɗa musu karin da taimakon Khadija ɗiyar Salamatu yariyar akwai nutsuwa atare da ita duk da baxata wuce shekara gomaba, sai ƙanwarta wadda suke sa'anni da Ismaha Zainab mai suna Hafsat, da ganinta bata ji, Babbansu shine mai shekara sha biyaar Usama wanda bashi da kirki asalima shine ya taso Ruqayya dan ta musu aiki ya kuma bige bakin Ismaha Zainab, wanda yake bin bayansa mai shekara sha biyu Musa yana da rashin ji amma kuma baya shiga sabgar da bata shafeshiba Khadija ke bin bayansa mai shakara goma sai mabiyinta Haruna ɗan shekata bakwai, Hafsat itace auta acikin ɗakin Salamatu.
  Rabi kuma yaranta na farko sunansa Walidi ɗan shekara shida sai qanwarsa Bilkisu mai shekara uku, Walidi baya ji sosai jan faɗa gareshi ga mugunta hakan yasa suke yawan faɗa da Musa yake dukansa, shi kuma sai ya huce akan Autarsu Hafsat, abin da yake kawo hargitsi kullum agidan sai anyi faɗa tsakanin iyayensu.

Bayan kammaluwar karin kummalon ta koma ɗakin salamatu "Yaya na gama, kizo ki raba." Cikin mamaki Salamatu ta jiyo tana kallon Ruqayya, dan azamansu da Rabi koda wasa bata taɓa cewa ta raba girkin data dafa tun farkon zuwanta gidan.
Kai ta girgiza ta tashi zaune tana fuskantarta "A'a kije ki raba abinki, ki warema kowa nasa."

  Murmushi Luyya tayi "Yaya ai kece babba ni kuma baƙuwa ce agidan nan ban san ya kuke rabonkuba, gadai shi can na gama dan Allah kizo ki raba zaifi wadata kowa."

Tashi tayi cikin sanyi jiki ta nufi waje tun aɗaki dama take jin qamshin soya doyar tasan zatayi daɗi, haka ta raba ta zubawa kowa dai-dai lokacin da yaran gidan suka fito tsakar gida, Ismaha Zainab kuma tana faman ƙunshe baki gudun kada tayi dariya duk da taga Salamatu tasa kaya ajikinta.

  "Luyya nifa na kusa makala amakalanta, ki kila yazakal yazo mu tafi." kanta ta shafa kafin tayi magana suka tsinkayi muryar zakar, da gudu taje ta taroshi tana murna zasu tafi makaranta.

Risinawa yayi ya gaida Salamatu ta amsa da ɗan fara'arta dan yaranta basu taɓa gaidataba, cikin sauri ta miqawa Luyya kasonsu "Gashi kiyi ki sallameta su tafi, gana Alhaji Kuma sai ki miƙa masa"
Karɓa tayi tana rusunawa to yaya, kallonta takai ga zakal ta miƙa masa "Maza ka kai muku ɗaki kuci, da sauri, kada ka biya surutunta ta makararku."
Murmushi yayi ya karɓa duk da aƙoshe yake amma yasan bazata bari yace ya ƙoshiba.

Yau agidan Alh. Isah ko wani yaro ya cinye karinsa yana santi dan akwai kulawa da tsafta shi kansa shayin ya samu qarin armashin kayan ƙamshi saɓanin abaya da lipton da sugar ake musu, haka doya da ƙwai itama babu ƙarnin da suka saba ji alokutan baya.

*****
Danne-danne yake acikin na'ura mai ƙwaƙwalwa can kuma ya tsaya cak ya ƙurama wani abu ido yana murmushi shi kaɗai, ido ya lumshe yana buɗesu aransa yana aiyana inama ace yana tare da wanan abun.
  "Musaddiq banga kana shirin tafiyaba? Duk da kasan gobe ne tafiyarka." Muryar Ummansa ta tsinkayi kunnuwansa.
Gabansa ne ya faɗi sam ya manta da batun tafiyar, kai ya dafe "Ya Rabbi" kamar an mitsineshi haka ya miƙe ya zari mukullin mota "Ina kuma zakaje ina maka magana?"

Bai juyoba ya ƙara ƙarfin takunsa "Wani abu na manta yana cikin kayan shirin tafiyana ne." daga haka ya fice apalon, fatan dawowa lafiya ta masa tana ƙara dai-daita zamanta akan kujerar da take zaune.

  Tafiya yake yana baza idanuwansa agefen titin dake Matsaro ko wasu yara yaga da unifoam yana ƙura musu ido, har ya kusan shafe titin, amma baiga abin da yake fatan ganiba, tsaki yayi ya buga sitiyarin motarsa, yana shirin juya motarsa, kamar ance ya kalli gefe ya hangosu su biyu suna tafe ita da yayanta sai surutu take tana tafa hannayenta, shi kuma yayan nata yana kallonta yana murmushi.

Tsayar da motarsa yayi agefe ya fito yana jiran ƙarasowarsu, basu kula da shiba har suka kusa wucewa ta gabansa, ganin da gaske zasu wuceshi yasashi buɗa muryarsa "Baby" bata jishiba tana ta faman dariya da tafa hannu, shima tsintar kansa yayi da murmushi yana jin daɗin ganinta haka "Baby" ya faɗa yana ƙarasawa kusa da su, cakk ta tsaya jin muryar da kamar ta santa da sauri ta juya tana kallonsa, hannunta ta riƙe akan haɓarta alamar tana tunani, can kuma ta sake kallonsa "Baki ganeni bane?" ya sake mata magana, sai alokacin ta ɗauki muryarsa ta faɗaɗa dariyarta "Laah Yazakal kaga ƙato mai mulyar yaran danake faɗa maka." ta ƙarasa maganar tana dariya wanda yasa zakar shima biye mata, hakan yasa Musaddiq kallonsu yana murmushi shima, aransa yana girmama shirmen da suke dashi ita da yayan nata.

🥀🥀🥀🥀🥀

_Ko wani abu yana da kyau dai-dai nasa kyan, amma acikinsa akwai wanda yafi ko wane kyau, bazance zai zama cikinsuba amma idan kuka kimanta girman tausasawar da take cikin aiki da abun ƙwarai da kanku zakuyi alƙalanci akan zamowarku fiye da kowa._

#Um Nass
#NWA
#cmnt share nd like
#Da amana

ISMUHA ZAINAB CompletedWhere stories live. Discover now