BABI NA 30

632 65 0
                                    

*🏌♀ISMAHA ZAINAB 💍*

©BY *😘Um Nass 🏇🏼*

Babi na Talatin (Page 30)

Naɗe wasiƙar tayi ahannunta sannan ta maida ita inda take, kallon sarqar tayi da kyau, ahankali sai ta ke jin xuciyarta na bugawa da qarfi kafin wani lokaci kuma tsoro ya fara shigarta.
Ido ta rintse tana karanto duk Addu'ar da tazo bakin ta. Sai dai babu wani alamu da ya sauya hakan.
Miqewa tayi tsaye tana riqe da kanta wanda take ji kamar zai faɗo saboda nauyin da ya mata, can kuma ya fara rinjayarta tilas ta tsugunna a qasa tana qara juye-juye, wani sauti taji mai qara da amo akunnenta, nan take ta rufe kunnuwan nata, amma kuma kamar ta kunna qaran ne sosai acikin kunnenta.

Kafin wani lokaci kuma jikinta ya fara karkarwa nan ta sulale qasa tana maida numfashi da qyar, har kuma alokacin kunnenta na rufe da hannun ta.

Shigowa ɗakin Luyya tayi, da sauri ta qarasa kusa da ita ganin yanda take jujjuya kai tana riqe da kunnen ta, girgiza ta take tun qarfinta tana kiran sunan ta"Ismuha Zainab! Lafiya kike."
Bata jita ba dan har yanzu kunnuwan ta na cike da ƙara "Hasbunallahu wa ni'imal wakil." Addu'ar da Luyyah tayi cikin jin tsoron abin da Ismaha Zainab take yi.
Qaran ne ya ɗauke cak akunnenta, ahankali ta ɗago daga durquson da tayi, kana ta sauqe hannun ta da yake dafe da kunnenta.
"Luyyah!" ta faɗa cikin muryar wahla, wanda yasa Luyya jin faɗuwar gaba, musamman da taga idanuwanta sun koma jajir da su.
"Lafiya kike?" ta aika mata da tambayar tana kafe ta idanuwanta.
Kai ta girgiza dan ko kaɗan ba zata iya tuna abin da take ji ba, sanan ayanda take jin laɓɓanta sun mata nauyi ba zata juri yin bayani ba.

Miƙewa tsaye tayi kamar zata faɗi, "Ya Allah!" ta faɗa tana jize bakinta.
"Mi yake damun ki ne?" Luyya ta aika mata da tambayar cikin tsoron amsar da zata fito abakinta, dan ayanda taga idanuwan ta da yanayin jikinta ya tuno mata da matsalar da take ta ɗawainiya da ita tsawon shekaru goma sha biyar da suka shuɗe abaya.

"Nima ban saniba Luyya, amma ina jin haushin komi da zai gifta agare ni."

Cikin tsoro Luyya ta fiddo ido waje, sanan ta miqe tsaye tana ƙara kai kallonta ga Ismaha Zainab "Kamar ya kina jin haushin komi? Mi kika fi jin haushi ayanzu?"
Kallon Luyya tayi sanan ta girgiza kai, tsugunnawa tayi ta ɗauko saƙon da Zakar ya bata, harda wasiƙar ta miqa ma Luyya "Shekara goma kenan tana jira nah, ɗazu ya Zakar ya bani amatsayin sauƙe nauyin da ke kan sa, sai dai ayanzu babu abin da na tsana kamar saqon da wanda ya aiko da shi."
Da sauri Luyyah ta buɗe ta karanta, kasancewar yanzu ta samu ilimi sosai ciki harda karatu da rubuta wasiƙa, saida ta karanta sanan ta kalli Sarƙar cikin tsoro da tashin hankali take juyata, tana kuma kissima adadin kuɗin da aka kashe wajan siyan ta da kuma girman wanda ya iya bayar da kyautar ta.
"Ya Allah!" Kalmar da Luyya ta faɗa kenan, cikin hanzari ta ɗauki wayarta ta fara lalimen wata lamba, sanan ta danna kira "Ina son ganinka yanzu nan." abin da ta faɗa kenan bayan an ɗaga kiran, sanan ta kashe wayar.

Zama tayi abakin gado tana dafe da kanta, tuna ni birjik marasa amfani ke ta safa da marwa acikin zuciyar ta, idan har akwai wani abu da yake da burgewa da kuma armashi ga rayuwar ɗiya mace budurwa to ba xai wuce wanan ba, amma kuma saɓanin tunanin kowa da jin daɗin su ga Ismuha Zainab hakan gazawa ce ko kuma baƙar duhuwar da take lilliɓe da ita ce take son dakatar da ko wani jin daɗi nata.
Numfashi taja ta fuzgar da iska abakinta "Ni banga wani abin jin haushi anan ba, idan har na fahimci wanan saƙon kamar tun kina ƙarama yake son ki, haka kuma yana son labarin ya riskeki alokacin da tunaninki ya kai ki auna fahimci zuciyarki." Luyya ta faɗa tana kallon Ismaha Zainab wanda ta zauna kusa da ita tana dafe da kanta.

Kai ta girgiza cikin nuna halin ko-in-kula ga maganar "Wanan shine babban kuskuren da nake ga yayi, duk da atsawon shekarun nan ina ganin kamanninsa suna xuwa min amafarki na har ma muyi hira, yanzu kuma da naga wanan tsohuwar ajiyar da sunan sa yasa ni jin tsanar sa, da duk wani abun da zai zo daga gareshi."
Mamaki ne ya kama Luyya sosai wanda ta gaza ɓoye shi "A mafarkin ki kuma?"
Kai ta gyaɗa tana murmushi "Eh!"
"Amma alokacin kina jin haushin sa ne?"
Kai ta girgiza mata "Ina son ganinsa ne awanan lokacin, har bana so na tashi abarci." sai ta ɗan yamitsa fuska kuma kamar taga wani abin ƙyanƙyami "Nifa na tsani ace ana SONAH Luyyah, amma kinga shima ya janyo na tsaneshi."

ISMUHA ZAINAB CompletedWhere stories live. Discover now