*🏌ISMAHA ZAINAB 💍*
©BY *😘UM NASS🏇*
®NAGARTA WRI. ASSOCIATION
BABI NA SHA TAKWAS (page 18)
Tsawon wata guda kenan yana ɗauko ɗan-akwatin da zummar ya buɗe, amma wata zuciyar na tsoratar da shi, tana tuna masa girman amana da alƙawalin daya ɗauka na cewa ita zata buɗe da hannunta.
Iska ya furzar abakinsa yana jin wani abu na yawo agame da ita da shi. _"Mi yasa yake kallonta? Rana ɗaya kawai ya sata farin ciki kawai dan ya ɗauketa ahoto."_ ya qarasa maganar kamar wani ke kusa dashi, sanan ya buga wani ƙaton tsaki.
"Wai kai lafiyarka ne Zakar? Kwana biyu na lura da kai ka fiya ƙunci da yawa." maganar mahaifiyarsa ta ankarar dashi akan abin da yakeyi.
Ashe kowa ya kula da shi "Ba komi Mama. Na matsu ne na gama karatuna na fara aiki, kinga sai ku aura min Ismaha Zainab?"
Ido ta ƙwalalo waje, cike da al'ajabi ta fara magana "Kai Zakar bana son shirmen banza kaji ko, har nawa kuke kai da Ismaha ɗin da zaka shiga wani batun aurenku da ita? Ko da wasa karna ƙara jin wanan maganar abakinka, dan zan sassaɓa maka."
Baki ya turo gami da kwaɓe fuska bai dai ce komiba dan yana shakkar Mamansa, sai dai aransa yasan bazai bari wani ƙato mai muryar yara ya masa ƙwaceba. Zai kuma dage yaci gaba da bawa Ismaha Zainab kulawa har zuwa girmansu sai ya sanar da ita.
******
MISRAH
JAMI'ATUL AZHAR
Ajin ne ya ɗauki shuru kamar babu wanzuwar bil'adama acikinsa, sai muryar malamin da yake ta faman yi musu karatu cikin harshen Larabci wanda daga ji yanda yake fiddashi kasan ya aikatu wajan fafutukar neman ilimi. Haka kuma ya alaƙanta matsayi biyun daya taka na zamansa mai ilimi da kuma haifaffan ƙasar laraba.
Bayan ya kammala ya buƙaci wani ya ƙara yin sharhin abin daya koyar dasu, shuru ne ya ratsa ajin har tsawon muntuna uku, can Musaddiq ya tashi ya fito gaban Ajin fuskarsa ko kaɗan babu fara'a, cikin muryarsa mai sanyi da amo ya fara jawabi fiye da wanda malamin yayi, nan aka shiga yi masa tafi haka malamin ya masa jinjinar yabo, ya ɗora da cewar kowa yake buƙatar bayani kai tsaye ya nufi Musaddiq zai fahimtar dashi, daga haka yasa kai ya fice acikin Ajin.
Tattaro litattafan sa yayi ya fice yabar ajin. Gindin bishiya ya samu ya zauna shi kaɗai, dan baya son hayaniya, haka baya son duk wani abun da zai hanashi jin daɗin tunanin da zaiyi.
"Ƙato mai mulyal yala" sautin maganarta yake ji acikin kunnensa, ido ya runtse yana murmushi "Mi yasa sai da lokaci ya ƙure min kika shiga cikin rayuwa ta? Nayi fatan ace kullum muna atare ne nida ke."
"Lafiya kake magana kai ɗaya musaddiq?" da sauri ya buɗe idonsa ganin Ma'aruf abokinsa ya sashi yin ɗan tsaki "Ka fiya takura Ma'aruf. Kazo ka katse min jin daɗina." ya ƙarasa faɗa yana ƙoƙarin ɗaure fuskarsa wanda tun da yaji maganar Ma'aruf yaji ransa yayi mugun ɓaci.
"Allah ya baka haƙuri Abokina. Banga jin daɗin da kakeba ne, dan nafi tsammanin kayi gamo shi yasa ka ware cikin mutane kake magana kai ɗaya. Na kula da ko wani motsi naka kullum sai ka zauna anan kana magana kana dariya. Anya bakayi gamo ba?"
Wata harara Musaddiq ya buga masa cike da jin haushin ma'aruf ɗin "Abin da yafi gamo nayi dai, ɗan sa ido kawai." Yana gama faɗar haka ya fara ƙoƙarin tattara littafansa zai bar wajan.
Da sauri Ma'aruf ya riƙeshi "Yi haƙuri abokina. Darasin malam khalil zaka min tuni dan Allah, sam ban fahimci komi aciki ba."
Hararsa yayi sanan ya zauna "Dama ina zaka sani hankalinka yana ga matan larabawa."
Dariya sosai Ma'aruf yayi bai dai ce komi ba har ya gama yi masa karatun Sanan yayi masa magana "Kai ai na lura kana da garanti auren gida za'a maka. So ni ka barni na bawa idona haƙƙinsa ƙila na dace."
YOU ARE READING
ISMUHA ZAINAB Completed
AdventureAbubuwa masu yawa sukan buƙaci tausasawa da killacewa ga makusantan su. Amma idan aka samu tsaiko da rashin su, sai asamu rauni da gajiyawa ga wanda ke ɗauke da jigilar hakan, wata ƙila kuma ya ƙare rayuwar sa cikin yaƙe ba dariyar dake wanzuwa daga...
