BABI NA 19

427 41 1
                                        

*🏌🏼‍♀ISMAHA ZAINAB 💍*

©BY *😘UM NASS🏇*

NAGARTA WRITERS ASSOCIATION

BABI NA SHA TARA (page 19)

Shuru ne ya karaɗe wajan can malamin ya juya yana kallon Ismaha Zainab da take ta faman ƙif-ƙifta ido "Amma dai kin san nan ba wajan wasa bane? A taƙaice kuna cikin aji ba a kaɗa muku lokacin wasa ba."

Baki ta cunno ba tare da tayi magana ba "Oya maza bashi haƙuri kafin na zane ki yanzun nan."
Shuru tayi bata ƙara tanka masa ba haka kuma bata da niyar bashi haƙurin. A zabure malamin ya tashi  kamar zai dake ta  "Yi haƙuli Abdul" ta faɗa tana ɗano baki.
Kai kalamin ya jinjina yana ƙara bawa Abdul haƙuri akan abinda ta masa, gami da cewa karya ƙara yin wasa a cikin aji.
"To", ya faɗa kana ya ɗauke shi aka saka masa magani da bandeji a wajan, a zuciyarsa yana cike da takaicin Ismaha Zainab gashi babu ko mutum guda da yabi bayansa asali ma kowa tsoron ta yake.

Aji suka koma aka ci gaba da yi musu darasi har zuwa lokacin tashi yayi aka tashi bata tankawa kowa ba. Sai a hanya ne suna tafe ta tare Abdul yana ƙif-ƙifa ido, sosai yaji tsoron ta ya kama shi duk da cewa ya girme mata amma kuma ta ƙware wajan mugunta. Cikin rawar murya ya fara magana "Ni ki barni na tafi gida, ai na bar yin wasan da ke."

Harara ta zabga masa ba tare da ta matsa daga kan hanyar ba "wa yace ka kai ƙalana wajan malam Kabil.?"
  "Ni magani naje a bani ba ƙaranki na kai ba."

Kan nasa ta kalla da yake manne da bandeji can kamar zata masa wani abu, sai kuma ya bata tausayi ganin yanda idanuwansa yayi rau-rau "To ka biyani haƙulin da na baka ɗazu."

Ai bai jira ta ƙarasa ba yayi saurin cewa "Allah ya baki haƙuri ƙawata Ismaha Zainab, Allah ya huci zuciyarki."
Kai ta gyaɗa cikin jin daɗin haƙurin da ya bata, sannan ta kalli su Asshe da suke jira tazo su tafi gida "Muje mu, kai kuma kalka ƙala min magana daga yau."
Kai ya gyaɗa yana fatan ta tafi dan zuciyarsa cike take da tsoro da fargaba. Yayi sa'a bata tsaya ƙara bin ta kansa ba.

Koda suka fara tafiya a hanya ta bugama su Khadija kashedi a kan karsu sake su faɗa a gida, dan idan Luyya ta mata faɗa zata huce a kansu.
Da sauri suka ce ba zasu faɗa ba. Ranta fal farin ciki ta tafi gida.

  ******
An dai samu sauyi da cigaba mai yawa a cikin rayuwar su Luyya da Ismaha Zainab, haka gidan Alh. Isah ilimi ya samu diga-digan zaman sa, ta yanda suke gudanar da kishinsu cikin sanyin hali, da wuya kaji suna sa-in-sa mai ƙarfi a tsakaninsu.
Shi kansa Alh. Isah ba ƙaramin jin daɗin zaman gidan yake a yanzu ba, wasu lokutan yakan Zauna yana bawa Abokanansa labarin yanda gidansa yake.

Sai dai fa har yanzu a ɓangaran Ismaha Zainab abubuwan ta na ruɗar da Luyya, dan duk lokacin da ta mata faɗa ko ta dake ta to a ranar bata samun cikakken barci, asali ma sai dai taji kanta na sarawa ko tana magana marar kai ita ɗaya, ko tayi ma mutum magana baya jinta.
Haka kowa a gidan yana shakkar shiga lamarinta ganin yanda take wajigasu idan sun so bata wahala.
Amma abun mamaki a makaranta bata taɓa ƙetare ta ɗaya ba, haka a Islamiyya tana da ƙoƙari mutuƙa, duk da ƙanƙantar shekarunta hakan baya hanata yin Hadda.
A haka ta kammala primary cikin nasara mai yawa da kyaututtuka daga malaman ta. Da yawa a cikin ɗalibai ƙanƙana suna murna sun rabu da jangwam uwar masifa. Haka suma malaman tasu murnar da alhini take tafiya, dan tana da ƙoƙari ƙwarai da gaske, takan ciyo musu kyaututtuka a sauran makarantu idan an haɗa gasa.
Haka a wajan rigima kullum sai ƴan ajinsu sun kawo musu ƙaranta.

*****
"Tabb wallahi bana son cigaba da wannan makarantar, haka kawai zan yi ta zama a waje ɗaya. Allah ni dai makarantar kwana zanyi, ai ance min can akwai daɗi ga abinci mai ɗanɗanon kaza, a banɗaki kuma harda famfon yima mutum tsarki."

  Tunda ta fara maganar bakinta ko kaɗan bai huta ba, sai dai ta samu tayi daga Khadija wanda take ƙaryata maganar tata "Ƙarya ce fa irin tasu Sa'adatu, har wata makaranta ce za'a samu famfon da zai yiwa mutum tsarki, banda rainin hankali."

Saurin buge mata baki Ismaha Zainab tayi, cikin jin haushin zata ɓata mata tsarinta ta fara kai kallonta ga Luyya wanda bata ma san tana yiba, dan cikin dake jikinta ya mata nauyi sosai, a shekara biyar a gidan Auren ta sai yanzu Allah ya ƙaddara samun ciki a gareta, bayan wahalar laulayin da tasha.
  "Luyya ni dai a kai ni makarantar kwana, ko kaɗan bana son makarantar jeka ka dawo."

Kai ta gyaɗa mata kawai dan bata shirya yin musu da Ismaha Zainab ba sanin ko taƙi ba haƙura zata yiba "Idan Alhaji yazo sai ki sanar dashi, amincewar sa akai shine nawa."

  "Ni dai bana son makarantar kwana wallahi, sai dai taje ita ɗaya." cewar Khadija gami da aikama da Ismaha Zainab da harara.

"Nima bana buƙatar naje da kowa, sai kuyi ta zama a gida ai."

Lokacin da Alh. Isah yaji batun makarantar da Ismaha Zainab take so, yaso ya hana ta amma ganin dagiyarta da kwarzana ihun data fara yasa shi cewar zai kai ta, ƙarin daɗawa shi asallarsa ko banza ya huta da bawa mutane haƙuri akan rafke yaran mutane da take yi.
Usama kuwa da ya samu labari har da rawa ya taka, asali ma shi ya karɓi kuɗin siyayya ya siyo mata kaya ragajab. Da taimakon wani malamin makarantar kwana Kamilu Ibrahim, Alh. Isah ya samawa Ismaha Zainab makarantar kwana ta ƴan mata dake Kaugama.

Ranar sai da Ismaha Zainab ta hana ɗaukacin ƴan gidan barci da murna da ihu, dan kullum tana gidan su Sa'adatu tana bata labarin yanda makarantar take, ƙara ƙawata mata daɗi da kyanta take yi. Hakan ya sata yin fankama akan ta kusa ta huta da cin Taliyar Luyya da ɗan-wake wanda ba ko yaushe ake sabunta musu abincin ba, tun wanzuwar fara ta.

****
"Ismaha Zainab ɗokinki yana yawa a kan wannan makarantar, amma ni Allah ya sani hankalina bai kwanta da tafiyar kiba. Ban sani ba ko wani alkhairin ne yake jiranki a can." numfashi taja ta fuzgar da iska mai ƙarfi a bakinta, cikin sanyin muryarta taci gaba da yi mata magana "Ina so kimin alƙawalin ba zaki yi shiririta a makaranta ba, ki kauda ko wani sabon abin da kika tadda a can mutuƙar bai shafi karatun kiba, ki gujewa afkawa ruɗin momyn makaranta zuwa ƙawa da ɗiya bayan ni da kika bari a gida."
Kai ta gyaɗa "Allah bazan yiba Luyya na miki alƙawari."
  Murmushi tayi, dan tasan tunda ta rantse to babu dalilin da zai sata aikata hakan "Ba ko wani abu bane yake da kyau idan an kalle shi, wani abun sai an zauna dashi a ke gane aibunsa, ki lura da kyau Ismaha Zainab idan a cikin tafiya babu guzuru mai kyau gundurarwa gare ta, ki kulle idanuwanki ki toshe kunnuwanki daga jin sauti da duhun da baya bada amo mai kyau. Ina daga nan zan cigaba da miki Addu'ar kariya ke ma kada kiyi wasa da Addu'a kinji?"
Kai ta gyaɗa ta rungume Luyya sai a lokacin nadamar barin ta gida yayi, kamar tace ta fasa amma kuma taya zata ƙi bayan akwai tarin abubuwan da suke jiranta na jin daɗi a can.
"Zan yi kewar ki Luyya. Amma nasan zan dawo na ganki da sabuwar ƙanwata."

Tana gama faɗar haka ta sake ta tana dariya ta ɗaga mata hannu, har ƙofar gida suka rakota kasancewar Alh. Isah ne da Usama zasu kai ta a motarsa.
Hannu suke ɗaga mata suna mata bye-bye.

🥀🥀🥀🥀🥀

*Rabuwa babu daɗi komi rashin daɗin zaman da a keyi.*

  _hhhh ga fa Ismaha Zainab a hanyar tafiya bodyn skull, ku hasko min rayuwar da zata fara ga sabbin mutane. Amma ai zata iske naman kaza da kuma famfo mai tsarki. Lol_
*GIRMAMAWA*

#Um Nass
#Cmnts. Like and share
#Da Amana

ISMUHA ZAINAB CompletedStories to obsess over. Discover now