43

13.4K 1K 179
                                    

             *RUMFAR BAYI*
          (A historical fiction)
Na Afrah bhai
Page 43

*KARSHE.........*

ONELOVE😘

********************

      "Washe gari...
Sai ga mai magani ta dira a cikin sashen sarki jalal..
Jalal ya saka jakadiya taje tayi masa kiran surayya da kuma juwairiya..

   Ai kuwa sai gasu sun shigo..
Surayya gaba daya jikinta babu wani karfi duk tayi laushi..
Jalal ya kalleta yace,surayya tunda kin ki sanar dani meke damunki yanzu dole ne ki tsaya me magani ta duba mana ke dan mu san halin da kike ciki..bakya ganin duk yarda kika koma ne?

Surayya ta shiga girgirza masa kai tana zubar da hawaye...tace
Sarkina nasha fada maka babu abunda ya ke damuna kada ka damu dani duk laifin da nayi muku....am...kuka yaci karfin ta..
Juwairiya ta dafa ta..a sanyaye tace..
Ah ah surayya ki bari kawai a duba ki dan hankalin mu bazai taba kwanciya ba idan har bamu san meke damun ki ba...

  Da kyal su juwairiya suka samu surayya ta yarda me magani ta duba ta..
   A firgice me magani ta kalli jalal tana fadin..
Mai martaba ai guba ce a jinin ta....

GU'BA!!!!!!
Jalal da juwairiya suka hada baki wajen fada cike da tsananin fargaba..
Ita kanta surayya sai da lumfashin ta ya dauke na wasu yan dakikai..

    Mai magani ta saka surayya ta kwanta flat a kasa,sannan ta saka wasu allulori ta tsaka su a saman ciki ta  sake fitowa dasu..
Sai ga wani bakin jini ya fito bakikkirin dashi..
Ta sake kallon jalal tace, Guba ce me tattare da bakin asiri,kuma tabbas da baku kawo ni nan yau din nan ba ina tabbatar muku da cewa a cikin watan nan zata iya rasa rayuwar dan bakin asirin dake jikinta ya gama gurbata jinin dake jikinta..

Jalal tashin hankali sosai ya shiga..
Juwairiya ma duk ta rude ta kama hannun surayya dake kuka sosai tace..
Dan Allah surayya ki sanar damu meya same ki?waye yake son kashe ki?
A ina kika ci wannan bakar Gubar?

Surayya duk a rikice take jin abunda me maganin nan ta fada..
Ta rirrike  juwairiya tana wani irin matsanan cin kuka...
Sannan ta sanar dasu duk abunda ya faru..
maganin neman haihuwa  ne da sukaje amsa a wajen wani malam can Sandamu,tunda tasha maganin ta rasa sukuni...

  Jalal  kam takaici duk ya ishe shi..
sbd neman haihuwa gashi nan  taje zata kashe kanta a banza..
Mai maganin tace..
Ni abunda ban gane ba a nan shine..
Shi me yasa malamin zai nemi ya kashe ki da bakar guda?
Bacin da kudin ki kika je wajen sa neman taimako..
Juwairiya tace nima shine na gani ai..
Ta kalli jalal tace..
Amale dan Allah ka saka aje a dauko mana wannan malamin ya fadi dalilinsa na son kashe surayya da bakar guba..
Jalal ya kalli jakadiya yace..
Kije ki sanar dasu shamaki aje can sandamun a dauko min wannan bokan malamin!!!..

"Malam sandamu a gaban sarki Jalal da sauran(royal family)...

Jalal ya kalli sarkin dorina dake tsaye yana ta bude hanci..
Yace..
idan har bai fada mana gsky ba akan dalilinsa na son kashe gimbiyar daura surayya.. toh na baka izinin lugwigwita shi a nan wajen..
   Malam na Sandamu ya hau wiki wiki da ido tsoro ya shige sa sosai..
Hamza yace..
Kayi mgn malam!!!!ko kaga tsararrakin ka a nan ne?

Malam ya zube kasa yana neman gafara yace..
Wlh tallahi babu ruwana a ciki..
Sarkin dorina ya kai masa duka mai shiga jiki..
Malam ya hau ihun azaba sannan yace..
Wallahi BAIWARTA ce,baiwarta ce wlh babu ruwana a ciki !!!!..

Jalal yace baiwarta ce?
Gaba daya wajen suka cika da al'ajabi da kuma tsananin mamaki!..

Surayya da kyal take iya bude ido ta kalleshi..
UMAYMA ta gama cutar  da ita..
har abada ba zata taba yafe mata ba..
Yanzu dama kashe ta dake da niyyar yi?
Lallai mutum abun yarda bane..

Rumfar bayi Where stories live. Discover now