Ido ta gwalalo tace ya Ahmad me kakeyi haka?juyowa yayi yace "morning wifey kin tashi lafiya?
breakfast nake hada mana kinga na kusa qarasa wa ,nasan kinajin yunwa koh ?"shi kadai yake maganar shi, Dan iman tama kasa ansa mashi tana tunanin yanda ya Ahmad yayi wannam aikin acikin ranta take cewa "gaskiya
Nayi dacen miji Allah na gode maka
"Ahmad Kuwa yanata aikin shi na kallon ta wanda yafi mishi Komai dadi ,
daga baya ya juya ya Cigaba da aikin dashi
indomie ce yake dafawa
taji da attarugu da Albasa ,da eggs .budewan marfin da yayi ne taji wani irin qamshi mai dadi ya ziyarci hancin ta shaqar qamshin takeyi sosai yayin da Ahmad ya sauke indomien ya dauko plate ya dauraye ya juye indomie din aciki itadai iman kallon shi kawai takeyi yanata faman fasa kwan daya dafa ya aza kan indomie din
, folk ya dauka qwaya daya ya aza saman plate din ya dauka yace "wifey ki jirani ina zuwa "ya fita da plate din ya ajiye akan dinning table din.saiya koma kitchen din inda yadda iman ta shiga duniyar tunanin .
Tana tsaye Sai kawai taji anyi sama da ita batasan lokacin da tayi qara ba ."ya Ahmad ni ka sauke ni zanyi tafiya da kaina "cewar iman cikin shagwaba Ina bubbuga kafa kaman yar yarinya 🥰😂🤣🤣Shi kuwa ya Ahmad ko kallon ta baiyi ba sai dinning ya ajiye ta ya jawo kujera ya zauna ,jawota yayi ya azata kan cinyar shi ya fara bata indomie din😋😋 lomar farko ta lumshe ido aranta take cewa "gaskiya ya Ahmad ya iya girki "
batasan ya ganta ba lokacin data rufe ido yace "Babe kodai abincin baiyi maki bane ?"cewa Ahmad ya tsareta da idanu
Murmushi tayi "sanan tace Wallahi ya Ahmad yayi dadi Asali ban taba cin indomie ne dadin wanna ba "
Murmushi yayi cikin Jin dadi sannan yace"Na Gode wifey"
Abinchi ya Cigaba da bata tare da tea
saida yaga ta koshe , sannan yace "oya it's my turn nima a bani naci "
fork din ta dauka ta fara bashi shima yanata kallon ta harya koshi sannam suka kwashe kwanukankitchen sukaje ,tana wanke wanke ,yana mata daurayan abunda suka bata......
Su ahmadu sakaran soyayyah ❤️❤️❤️❤️❤️💃💃💃💃💃Parlor suka dawo Sai kunna masu kallo iman tana zaune a doguwar kujera Ahmad ya zo kusada ita ya kwantar Da kanshi bisa cinyarta .
Kunna tv yayi ya saka tashar Hausa TV , Tafseer akeyi, na malam kabiru Gombe akan aure ,ahankalinsa yamaida kan tvn.
Itama iman saita maida hankalinta akan wa'azin.
Sai kusan 12:00 aka kammala tafseer d'in, ya Ahmad yamik'e yana fad'in Alhmdllh, Malam mungode, ALLAH yabiyaku.
Tashi ya Ahmad yayi ya wuce daki iman kuwa
Kitchen ta wuce ta fara kokarin daura abinchin rana sai ga Ya Ahmad ya dawo ,kitchen din ya buyo ta,yana taimaka mata jollof suka dafa da kayan ciki tanata qamshi mai dadi suka kwashe a Warmer's masu kyau suka jera a dinning kowa dakin shi ya koma danyin wankakowa wanka yayi Ahmad ya fita masallaci domin sallar azahar itama iman wanka tayi tasa doguwar riga marar nauhi sabida zafin da akeyi rigar tata red mai ratsin ash tasa hula mai kyau itama red tayi light make up tayi kyau sosai Masha Allah😚 sallah tayi ta fito parlor fitowar ta keda wuya saita ji an bude kofar shigowa ya Ahmad ta gani ya shigo mamaki ya kamata ganin shi da riga red shima da wando ash kamar hadin baki sunyi kyau sosai.
Kara sowa yayi yace "wow sweetheart kinga yanda kikayi kyau kuwa gashi kinyi mini copy copy"cewar Ahmad ya daga giran yana kashe mata ido
kunya ce ta kama iman ,tayi maza ta rufe fuskar sannan tace "niba wani gasar ka da nayi ya Ahmad kaine dai kayi mun copy copy "cewar iman cikin shagwaba
Dariya sukayi duka ,Sai ya Ahmad yace "wai ni bazaa dena cemin wanna ya Ahmad din bane "ya fada cikin zolaya"Uhm uhm uhmm, ni me zance maka ,bansan sunan da zan ringa ce maka ba "cewar iman duk cikin shagwaba
Shi kuwa goggan ya fara rasa natsuwar ,Sai kawai yace "Haba yan mata kizo na fada miki "
Ita kuwa a nata tashin wayon ta tashi taje "
aiko ya Matseta ,tana ta neman hanya guduwa ta kasa ,
Yace mata "kinason na sake ki ?"cewa Ahmad
Haba ta matsu cikin sauri tace "eh"Dariyan mugunta yayi sanna yace "ki dena cemin ya Ahmad ,suna me dadi nake son ki saka mun"
ya Ahmad yace mata yana dariya kasa kasa was poo tare da daga Gira daya
Girgiza Kai tayi tana futar da numfashi kadan kadan tace "na dena nisful qalbi "ta fada da kyar tsabar kunyaWani dadi ne ya Kama Ahmad yace ta kuma maimaitawa ,maimaitawa ta kuma yi ,
Aiko rumgumeta yayi ya dagata sama sai dinning area
Kujera ya ja ya zauna ya daurata akan cinyarsa
Plate ya dauka guda daya da spoons Guda biyu
iman ta bude Warmer's din qamshi ya bige ko ina nima kaina saida na hadiye yawu abincin suka fara ci yana bata tana bashi har suka qarasa......*Bayan sati daya da aurensu*
Iman ce ke shara Ahmad na mata mopping suna ta sauri suyi su gama su daura abinchi ,saboda suna da baki yau kannen Iman ce zasu zo daga gora
Sun gama gyaran gidan suka wuce suka daura abinchi suna ta fira abunsu gwanin shaawa ,abun birgewa kuwa .
Suna gama aiki zasu je yin wanka ,Ahmad ya Kafe ma iman wai tare zasuyi wanka

YOU ARE READING
sabuwar rayuwa
RomanceIt's all about love, destiny,and fate. life is not always a bed full of roses......