Sallama tayi cikin gidan mutane Sai amsawa sukayi suna kallonta ,da mamaki fal a zuciyar yadda iman ta koma kamar wata baturiya ga wani uban genza da ta saka a jikinta , gashi taui kyau ,skin dinta dai Kelli yake ,tana taku kaman wata sarauniya .
Gaishesu tayi cikin daddadan murya ,
Wasu ma basu samu natsuwar amsawa ba .........
A cikin Yaran gidan sai kallonta suke , kowa burinsa yay mata ta amsa ,yaran gani suke kaman ba Yayarsu bace .Ita dai iman bata kara bi takan matan gidan ba ,wucewa tayi dakin hajiyarta ,
A dakin hajiyar ta tadda auta ma , hand bag da gyale dinta ta ajje ,ta zauna suka gaisa da hajiya sosai
Fira suke yaushe gamo.......Abinchi aka kawo masu ,shinkafa da wake daga gidan hamma ,Amma ita Iman tace Tuwon dawa zata ci ........
Adda Halima dake mata wani kallon sama da kasa suka kwashe da dariya ita da Zainabawa da hafsatu.
Hararsu tayi cikin wasa, "malamai lafiya?".
Cikin dariya adda Halima tace "Ashe kina cin Tuwon dawa😂🤣😂"
Kallon su zainabawa tayi da hafsa suka dena dariya tunda sun san haliKallon adda Halima tayi tace "kawia shi nake son ci "
Hango bilkisu da ke wucewa tayi Ka kirata "Keesu Tuwon dawa nakeso miyar kuka ko kuɓewa ɗanya, asamo yajin daddawa da manshanu".
"Naga ta kaina, Adda iman wannan lissafin fa? To bara nakaima yaya Ahmad fura na dawo".
"To maza, idanma babu manshanun a aika gidan ardo karami nasan baza'a rasaba".
Fita bilkisu tayi tana amsawa, yayinda su Adda Halima suka dasa sabuwar dariya.
A haka anty Amarya ta shigo ma Iman da tuwon dawa sai tururi yake, "Iman ga tuwon, ga bilkisu can zata soya miki man shanun".
"Lah anty na sakaku aiki, maimakon kubar zainabawa ko hafsat suyi".
Dariya anty amarya kawai tayi ta wuce ....
Ba Iman kawia ba har su adda Halima sunyi mamakin Sauyawan anty Amarya ..
Shigo da man shanun da bilkisu tayi ne yasa babu Wanda yace komai ,
Zama Iman tayi za labci abinchin ta .kowa sai kallon Iman yake, komai nata birgesu yakeyi, kallonta suke tamkar wata sabuwar halitta daban a cikinsu.A cikin kananun maganganu na mata Iman taji abinda ke faruwa ,abunda ya faru da Baffa ardo ,wannan abokinsa wanda yaso Iman ta aura ne ,ya damfaresa
Yasa baffa ardo hada duka dukiyarsa wai zasuyi Sana'a dashi ya hade ya gudu dasu gaba daya .Gashi ya gudu ya bar mata guda shida da 'ya'ya 36
Ga tashin hankali , idan anyi sata a unguwanan 'ya'yansa ne ,ko shaye shaye ga mugun caca ,subhallahi rayuwan 'ya'yansa sai a hankaliAllah sarki Iman har da kwalla ,sun bata tausaya,Alhamdullah ta ringa fada ,da tana tunin tana cikin wanna masifan 😭😭😭
Shi kanshi Baffa ardo ,tsabar tashin hankalin har dena gani yayi ,abinchi Sai an dafa a nan gidan zaa Kai ma gidansa , munafukan matansa masu zugashi duk sunyi sanyi babu da Komai yanxu
A haka dai iman ta yini babu inda taje ,Dan Ahmad yace karta futa wannan zuwan saboda baba sukayi shi .
A haka dai suka yini sai 5 suka shirya zasu tafi , Amma auta bata nan ta raka zainabawa cikin unguwa ,suna tsaka da jiranta Sai gata ta dawo
Suka wuce gida..........

YOU ARE READING
sabuwar rayuwa
RomanceIt's all about love, destiny,and fate. life is not always a bed full of roses......