page 2

423 31 2
                                    

Misalin karfe 6:00 na yamma motocin daukar amarya suka fara layi mata suna sauka amare hudu kowacce ankawo su za a kaisu dakin Hajiya abada amanarsu kafun akaisu dakunansu anzo kofar shiga Fatima ta takewa Nusaiba kada ta murje kafar sosai saida Nusaiba tayi kara ranta yayi mutukar bace aikwa batayi wata wataba ta cire mayafinsa ta kwadawa Fatima mari." Kan uban can nikika mara to wallayi saina rama bazan yaddaba." tacire mayafinta itama ta yi damara suka fara kokawa suma danginsu suka kama junansu da kokawa.

Zabba'u tayi gefe tatsaya tana yatsina fuska tace." Dukkan su mahaukatane wallayi,Allah ya hadani da kishiyoyi,masu mugun,hauka zanyi maganinsu wallayi sha sha shai." Sadiya tana kusa da ita bata saniba ta kyabe baki." Duk inda talaka take saiya nuna halinsa koda yake mai dattin hula baisaba yiba uwalle batayi." nan take Zabba'u ranta yagama baci ta juyo ta cakumi huyanta." Dan ubanki nizaki zaga bansa kemashashiya mara mamara to wallayi,saina yi maganinki,anan gidan." aikwa suka fara kokawa wata tayi saurin zuwa ta janyo hajiya." hajiya kizo amare da masu kawosu sai fada sukeyi sunki su daina." da sauri tatashi tafuto daga uwar dakin dama tafara jin haya niya tadauka duk shagalin bikinne.

Tana zuwa tsakar gidan taga amare sai fada suke da junan su yan uwansu suma sunkama yan uwar wasu suna ta kokawa wasu kuma suna ta kokarin rabawa hajiya ta kidimi tarasa yadda zatayi." Wai mene ne haka bazaku bari ba ina magana." ai bawanda yasan mai hajiya take cewa cikin bacin rai tayi gun su Fatima tana kokarin rabasu basu kota kanta basu biba suka doke doke suna zagin juna Fatima takawo duka tasamu hajiya jikuke dimm abaki sai jini,baahiri hajiya tasake tala ihu amma ko ajikinsu fadansu kawai,sukeyi ita kuma tarike gun tana ihu Hannutu ce tazo tariketa." Hajiya kizo mutafi daki,karsu illata ki muje daki sai in kira yaya awaya suzo su raba fadannan." kana hanunta tayi zata kaita daki wata ta nemi abokiyar fadanta tarasa ta dauka hajiya ce aikwa ta cakumeta da kokawa tahau dukanta kota ina.

Saikuma ihu yafara tashi mata suna zubewa suna tada aljanu hankali,mutane yayi mugun tashi hajiya jiki yasha duka kawai saita saki kuka." Wai wane bala'i na jajibowa kaina ni wannan aure wallayi dama za afasa kowacce ni tatafi gidansu nafasa auren." bawanda yasan sunayi anata kokarin yiwa masu aljanu addu'a amma wasuma zubewa zuke yi ciki kuwa harda amaren duka zabba'u tayo,kan hajiya cikin wata murya tace." ke ce wannan muguwar matarnan ko kince Husaifa baze aureniba ko to wallayi zan yi maganinki" cikin rawar murya hajiya tace." kinga yara ai ansaura nuku aure yau muje in kaiki dakinki ma kinji tawan." wata danka tayiwa huyanta mutane sukayo kanta suka kokarin kace hajiya.

SURIKAR MUCE Book 1Where stories live. Discover now