🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩*
*HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡
*NA: SLIMZY✍🏼*
_Wattpad@slimzy33_
*Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki**SAKO DAGA KUNGIYAR HASKE WRITERS* *ASSOCIATION💡*
*ZUWAGA DUMBIN MASOYAN MU MUKE SHAIDA MUKU WANI BAKON AL'AMARI DAGA MAHASSADA*, *AKWAI WANI SABON LITTAFI DA SUKA KIRKIRA ZAKUGA A SAMANSA AN AMBACI ...BILLY* *GALADANCI (MAGAJIYAR KARUWAI)....TO BA WRITE UP DINMU BANE BA RUBUTUNTA BANE ANYI HAKA NE DOMIN A BA'TA SUNAN TA, SHIYASA MUKA YANKE HUKUNCIN SANAR DAKU DA WURI KAFIN LITTAFIN YA FARA YAWO....* *BABU RUWAN BILLY GALADANCI DA WANAN RUBUTU BA NATA* *BANE....MAHASSADANE KAWAI...*
26
Motoci suka shirya tsaf da Yan rakiyarsu suka nufi gidan sarki cikin mintuna da Basu wuce arbain ba suka Isa....
Tun daga nesa Fatima ke hangen motoci na shigowa kasantuwar Tana can baya inda ake jibge Kaya idan ankawo Tana kwashewa Tana kaiwa dakin tsohuwar ajiya tun Daren jiya take aikin Abu daya har bacci ya kwasheta a wajen ta Dora daga inda ta tsaya da safe......
Hagensu takeyi suna tafe suna tunkaho Yan rakiyarsu na biye dasu haka dik inda suka wuce maaikata na zubewa a kasa suna kawo gaisuwa Babu Wanda suke kalla ballantana su amsa har suka shiga sashin cikin gidan.....haka kawai Fatima ta tsinci kanta cikin matsananciyar faduwar gaba.....ta Dade a tsaye Tana tunani kafin daga bisani ta cigaba da aikin da takeyi....
Bangaren hajiya babba suka yada zango tayi musu tarba Mai kyau Nan bilkisu ta shiga kawo musu kayan motsa baki Tana jerawa,
Sai wani Shan kamshi deejahmah takeyi Tana yatsina fuska...
"Hajiya barka da tashi Kinga nayi zuwan sassafe ko?"
"Ehh wallahi kin rigani zuwa ne Amma nikaina yau nayi niyyar shirya zuwa gidan naki'
"Muhimmiyar magana ta kawoni hajiya,wani mugun labari mukaji a bakin wanan jairin yaron kabiru har yasa deejahmah kuka"
Girgiza Kai hajiya babba tayi hade da yin murmushi Mai ciwo ta cije bakinta sanan ta fuskanci hajiya rahina "wanan maganar ki dauketa a ruwan kwando Domin harabada kabiru bazai auri shegiya Mara iyayeba"
"Cewafa yeyi yakai maganar gaban sarki....hmmm hankalinmu ba karamin tashi yayiba shiyasa na yanke shawarar zuwa gaban sarki infada Masa cin mutuncin da kabiru yazo har gida yayi Mana"
Kurriii da ido bilkisu tayi Tana kallon bakin kowa a cikinsu karaf sukai Ido hudu da deejahma a hassale tace'ke ubanwa kike kallo haka munafuka?tashi ki fita waye ya baki izinin Zama muna magana kina kallon bakinmu!"
Haushi ya Kama bilkisu Amma hakanan ta durkushe a gabanta Tana fadin "tuba nakeyi ranki ya dade waneni da shiga huruminku iyayen gidana"
Harara deejahmah ta wurga Mata ta nuna Mata kofa "tashi ki fita"
Sumi Sumi bilkisu ta Mike ta fita badan ranta yasoba.....
Ajiyar zuciya hajiya babba ta sauke "deejahmah kada hankalinki ya tashi Domin Nina tanadar Mata azabar da dakafafuwanta zatabar gidan Nan Domin yanzun haka tana can baya wajen ingiricin Doki nasata kwasar kayan da sukafi karfinta ta Gama in cigaba da azabtar da ita'
Askar dake boye cikin Jakarta deejahma ta Ciro Tana jujjuyaya "hajiya Kinga wanan askar?"
Hajiya na fuskatar deejahma ta amsa Mata da Kai "ehh Ina sauraronki"
"To da ita zanyi Mata azaba sanan zan aske kanta tsaf da ita Kuma in Zane Mata fuskarta da ita tamkar bayan kwarya"
Dariyar mugunta hajiya babba tayi Wanda rabonta da yinta har ta mance "lallai yata kinsan kan mugunta,....sanan nayi Miki alkawarin bayan kinyi Mata wanan azabar nikuma yau zan turata dakin tsohuwar ajiya a can zata kwana zan hada baki da daya daga cikin dogaren gidan Nan ya shiga ya far Mata cikin dare yayi Mata fyade,ya tabbatar yayi Mata kaca kaca yadda bazata moruba"
![](https://img.wattpad.com/cover/191531360-288-k885650.jpg)
YOU ARE READING
Anyi Walk'iya.......
Historical FictionBanida wata alak'a da Zina da zan aikata Shi Maryama,sabida na taso na Kuma girma acikin gidan marayu bashi ze bani damar wulak'anta ni'imar da Allah yamun ba ya tasheni acikin musulunci, menene aibuna Dan kawai nataso banida gata se'a hannun gwamn...