33

1.4K 99 2
                                    

🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩*

*HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡

  *NA: SLIMZY✍🏼*

_Wattpad@slimzy33_
*Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki*

     *_Allah ya maimaita Mana ya Kara Mai maita* *Mana shekaru_ _masu yawa_* *EID MUBARAK*

    _Anty rabi sakonki ya iso gareni nagode sosai Allah ya saka da alheri..._

                  33

Cike da natsuwa ta shiga dakin yayinda zuciyarta ta tsananta bugawa,fargabar abinda zai biyo baya takeyi Dan batasan laifin da tayiba ake Kiran nata...

   Gefe kadan ta tsugunna hade da sunkuyar da kanta kasa,..zuciyarta na tsananin bugawa ta bude baki a hankali tace "gani ranki ya dade ance kina nemana"

   Hajiya zainab wadda ke gefe ta kafe Fatima da Ido tunda suka shigo take binta da kallo har ta nemi waje ta tsugunna,...kallon yadda kayan jikinta sukai makal makal takeyi saboda datti sanan ta maida dubanta ga fuskarta wadda take a sunkuye ta kafeta da Ido....

  Shigowa dakin yasa dukkansu suka daga Kai su kalli waye ya shigo Babu ko sallama bare neman izini,

  Deejahmah Bata damu da wadanda ke wajenba Dan batasu takeyi ba Fatima kawai takeso ta ciwa mutunci saboda yadda idonta ya rufe,....tsaye tayi Akan Fatima hade da rike kwankwaso jikinta har rawa yakeyi savida masifar dake cinta,

  "NA aika akiramun ke shine kika dawomin da Yar sakon kikace bazakizo ba saboda ninayi Kama da Saar ubanki?shegiya har ta Kai matsayin da Yar sunnah zata kirata tace bazatazo ba?ko kuwa aikin bautar da kikeyi an yantaki ne?"cikin tsawa take magana,

  Bude baki hajiya karama da hajiya zainab sukayi suna kallon ikon Allah,

  Dakyar Fatima ta hadiye wani mugun miyau na bakin ciki sanan tace cikin sanyin murya "kiyi hakuri lokacinda kika Aiko kirana,Nan anrigada an Aiko kirana ko kafin tazo shiyasa nace Mata tace Miki zanzo idan nazo Nan naji Kiran da akemun"

Fincikota deejahmah tayi ta baya ta Fadi kasa,da sauri hajiya zainab ta Mike tsaye cike da masifa "dakata Mara kunya,kibari idan tazo saikiyi Mata cin mutuncin da zakiyi Mata Amma baa gabanmu ba wallahi tunda rashin kunyarki takai kishigo Mana daki Babu ko sallama,sanan ki rufe idonki kina kokarin ciwa Yar mutane mutunci to baki isaba kinyi kadan Khadija ai mafarkina be taba bani fitsararki ta Kai haka ba,Dan haka ki bacemun daga gani tun kafin nawa borin ya tashi insauke akanki"....

  Takaicine ya lullube deejahmah wani kululun bakin ciki yazo ya tokare Mata wuya Wanda yasa idanuwanta suka rufe ruf saboda tsananin bakin cikin abinda hajiya zainab tayi Mata gaban Fatima Amma dikda haka be hanata bude baki tayi magana ba

  "Ummu karya takeyi tun dazun na aike kiranta Taki zuwa saboda ni ta rainani shiyasa"

  "Da kika aika kiranta batazoba sai kika shigo Mana ko arzikin sallama bamu samuba ballantana gaisuwa dagani kuwa har uwar mijin Taki Anya Khadija wannan halin naki Zaki canjashi kuwa?rahina tayi Miki muguwar tarbiyyar da sai kinyi danasani Mara amfani a rayuwarki Nan gaba kadan,ki bacemun daga gani tunban gaggaura Miki Mari ba Mara kunyar banza"

  Jikin a sanyaye deejahmah ta juya batare da tace komiba zuciyarta nayi Mata suya,Bata da wani damar daukar hukunci a gaban ummu saboda sanin halinta Bata daukar raini haka ta fice cike da takaici,Mai makon tayi sashen da friends dinta suke sai tayi sashin hajiya babba.....

   Juyowa hajiya zainab tayi tana zazzaga masifa "wallahi wanan yarinyar da ake Shirin aurawa kabiru an hadashi da aiki,Domin batada tarbiyya ko kadan tun suna yara nasan halin deejahmah Bata laifi komi tayi daidaine a wajen rahina,banji Dadi ba ko da can da akace zata auri habibu balle yanzun da lamari ya juya Kan kabiru mutumin kirki"

Anyi Walk'iya.......Donde viven las historias. Descúbrelo ahora