💗💗💗💗
KAUNACE Sila
💖💖
💗💗💗💗💗AISHA A. BAGUDO (MMN SUDAIS)
Page 58
Cikin matsananci tashin hankali yakoma bakin kofar Amman yakasa tsayuwa sakamakon jiyo sautin kukanta dayajejiyowa a kunnuwansa" zuciyarshi tayi rauni tashiga rashin natsuwa , fuskarshi yasa cikin tafin hannushi yana sauke hadiyar zuciya numfashi yake ja ahankali yana fitardashi "yarasa mayyasa bayasan ganinta cikin damuwa balle wanna dayasan shine sanadi " waje yasamu cikin kujerun falon ya kwanta ya runtse idanunshi , kuka take tana bubbuga kofar tanakiran sunanshi wlh Khalid kazo kabudeni tun kafin na balla kofar nan mugu kawai macuci mai kan maciji sai Allah yasakamu tasake fashewa dawani sabon kukan ,sai da taci kukanta ta koshi sannan tasoma cire kayan jikinta tana watsarwa akan gado ta nufi bathroom tana zaginsa duk zagin da take aikomasa dashi yanajinta murmushin gefen baki yayi yana ciza lip's dinshi ,mikewa yayi yashiga dakin ya tadda mukifat ta fito daga wanka ya kalli agogo yaga biyar sauran minti goma, takasa karasowa cikin dakin dan towel dinshine a jikinta bataso yasameta haka ba, ita yake kallo yana takowa inda take tsaye juya tayi da sauri zata koma cikin bathroom taku daya yayi ya damko hannunta ya juyo da ita cikin zafin rai suna fuskantar juna ya tsareta da manyan idanunshi ,take yanayinsa yacanza zuwa bacin rai yace wakike Kira da mugu Ina wasa dakene koni sa'anki ne? cikin rawar jiki tace A'....a...nibada kai nike ba , yace Allah ko yasake matsota, to dawa kike har dacemin macuci ko ,to sai kingayamun cutar me namiki tayi shr yace OK bazakiyi mgn ba cikin matsananci tsoro tace karabudani wai me na tsaremaka ne dan Allah "yace abubuwa dayawa ciki har da zamanki cikin gidannan , yasa kafarshi yatake mata yatsu kafa tasaki kara wayyo kayi hakuri Allah bazansake zaginka ba, kima sake jikinkine zaiyi bayani ,kuma har da cemin maikan maciji cikin nidake waye mai kan maciji da sauri tace ni.....ce mai kan maciji Allah kuwa bada kai nike ba, wayyo kafata hawaye takejin suna sauka a sillin kumatunta tanajin duminsu har saman labenta cikin kuka tace nidai kafita hanyata yace in naki fa , ko akwai abubda zakiyi ne ta girgiza kanta " yace ok nadauka ko akwai matakin dauka ne mara kunyar karya kawai, yaja Karan hanci basake kallonta ba yashige bathroom ko me ya tuna sai kuma ya fito da sauri ita ko har ta Isa kan gado tasa hannu zata dauki kayanta tasaka takoma dakinta tunda yagadamar bude dakin ,yakaraso kusa da gadon shima yadaura hannu kan kayan yayi hanyar bayi dasu ya bude washing machine ya jefasu ciki sannan ya rufe kofar bayin duk tana kallon abubda yakeyi taji kmr tasa ihu " dan tasan tsabar iskanci ne kawai yakeson mata ,ta kalli towel din jikinta cikin sanyi jiki takoma dakinta tashirya tayi sallah ta nufi kicin , koda yagama yaje dakin ta Bai ganta ba ,ya nufi kicin can yasa meta tana hadamusu abinci yakaraso kusa da ita yana kallonta yace ke a gidan Ku ba koyamiki tarbiya bane tayi banza dashi wa zai gyara min dakina dakika bata ,ta tabe baki bata ko kallesa ba bare ta amsa ,kmr zaiyi magana sai kuma yafasa ya matso dab da ita ,yace kishiryawa rashin mutunci su Maryam da khadija dan kadan ma kikasoma Gani tunda kika nacewa aurena, hop dats clear tayi dariya batare da tace komai ba ,ta watsa masa mugun kallo ta juya zata fita daga kicin din yakamo hannunta cikin nashi yana murzawa yana kallon kwayar idanunta dauke kanta tayi,y yasake matso yashige jikinta har sunajin hucin juna yace in kunne yaji jiki ya tsira, ya matse mata hannu, idanunta ta runtse dan azaba sannan yabar kicin din taci GABA da aikinta koda suka gama cin abinci barin gidan yayi ita kuma taje tayi wanke wanke .
Mukifat na kwance a dakinta da daddare yashigo tanajin ya bude dakinsa yashiga" ta mike zaune ta rafka tagumi tana nazarin abubuwa da yawa har yanzu takasa gasganta wai Khalid ne ke mata irin wanna wulakanci tunanin haka yasa hawaye ya cika mata Idonu, tannan zaune har kusan 2 dare barci ya kaurace mata tara yadda zatayi da rayuwarta koma yagama cakudemata juyi kawa take akan gado tashi tayi a sanyaye tashiga bathroom ta dauro alwala ta fito tafara sallar dare .ta Dade zaune tana lazimi sannan ta koma ta kwanta .
YOU ARE READING
KAUNACE SILA
Romancekaunace sila all talk about ,neglect of parent, true love, parental obedience.