Najmah
Story written by
DielaIbrahim ✍️
(37)
****************
Ikleemah ta cigaba da cewa Mamie
Har Nijar nabi Abba lokacin daxai kaiwa khadeeja sako
Nayi magiya Amma ya ki saurare na.....sai nayi kakarin sa mashi kayan maye a abin cin shi don na samu yanda nake so
Tabbas yaci abinci Wanda daga restaurant din dayayi ordering
Aka kawo Masa Amma sai da na biyasu kudi kafin suka xuba Masa a juice
Sai dai Kash khadeeja ranar ita ta taimakeshi ganin irin halin dayashiga na maye
Ban samu nasara ba saboda ta dauko likita da Nurse Wanda su suka tsare shi har safiya
Nayi matukar bakinciki da hakan shiyasa na tsani khadeeja na tsani jininta
Uhmmmm Mamie Tai murmushi tace bamu da hakki akanki shiyasa kika kasa cin galaba akanmu Kuma dayardar Allah sai Kinga sakayyar abinda kikayi
Maxa ki fitan min daga gida Kuma Ina horonki da karki sake shigo min gida
Mamie da Bata fada Amma har waje ta fitar da ita sannan tasa masu gadi da karsu Kara Bari ta shigo gidannan
Mamie takoma Taki ta samu Abba tana kuka tana bakin ciki da irin rayuwar da ikleemah ta daukan wa kanta tun tana karama
Abba yaita lallashinta
Yace Mamien Yara kin kasance mace mai hakuri
Mamie Hakika idan mutun yasamu mace irinki to babu abinda xai yi saidai yai ta godiya wa ubangiji
Kinzama uwa Kuma uba agareni sannan kin haifamin ya'ya Kuma kika musu tarbiya Mai kyau
Babu abinda xan iya cewa lokacin da ikleemah tai min sharri acikin gidana, bani son hada ki da yar'uwarki
Shiyasa ranar da tace nine mahaifin Najmah
Kawai nai Mata Shuru don ban shirya fallasa sirrin ta ba
Amma Alhamdulillah tunda yanxu ta wankeni a wajen mamata mafi soyuwa acikin Raina
Mamie Tai murmushi tace Allah ya qara maka lafiya Abban Yara
I'will remain loyal sir till death
Abba yai Shuru Yana kallon Mamie
Hakika Mamie ta dabance acikin mutane da Kuma mata
..............
Da murnar su suka sauka a qasa Mai tsarki
Sun Isa masaukin su
Kowa ya nufi dakin da yake so
Fayrouz, Sadeeq da Shariff
Suna ta shawarwari akan yadda xasu bullo wa al'amarin
Sunan Wanda ya bani bayanai akan Marshal
Captain-Ibrahim Kuma
Suna aiki nee a qarqashin Marshal
Kuma yace a gobe Marshal xai iso Saudi,don Haka shi xamu bi
Saboda shine tiket dinmu na ganin Marshal
Ba gobe zamu ganshi ba
Ayanda plan dinmu yake dole mu jira nadan kwana biyu
Ina bazai yuwu ba idan yaxo yabar qasar fah
Cewar Najmah da take gefe tana sauraransu hankali a tashe
Su ka kalli Fayrouz
Alamar shi xai kwantar mata da hankali
Fayrouz ya tashi ya riko Mata hannu sannan suka Dan fita waje ta corridor suka tsaya
Yace mi Dil
Calm down kinji
Haduwa da Marshal ba karamin Abu bane ayanda yake da mukaminnan
Kinsan sojoji in mukaje Kai tsaye wlhy sai sun illata mu
So su suna son respect Kuma suna son mutun yabi order
Shiyasa zamubi komai ahankali kinji
Toh Yaya nagode
Toyi dariya Mana
Murmushi kadan tayi sannan suka koma daki
Ya xauna suka cigaba da shawara ita Kuma ta wuce daki
Ta samu su Minal suna kallo
Guys kallo kukeyi ahh Kuna shanawa
Ilham tace series nee wlhy
Yaya dai sun game plan din
Not yet
Ohk tih shikenan
Itama xaunawa tayi tana kallon Amma hankalinta Yana wajan mahaifinta
.............
Bayan kwana Daya Naj da Ilham+ Minal suka dauki mota suka fita
Yawan shakawa sunje Masallaci Naj tayi addu'a sosai Wanda sun dade suna zagayawa
Yamma likis suka Kama hanyan dawowa gida
Amma Naj taga ana saida wani abin wasan Yara Wanda su Suhaila da khaleel suna so
Abba ya taba siya masu da yaxo makka
Suka lalata Ya Fayrouz so nawa Yana siya su Kuma suyi ta kyauta dashi Wai Yara suna so
Minal kuntsaya insiya ma su khaleel wancen abin tsaraba
Minal tace abinda suke kyautar wa eh sai mu siya da yawa yanda xasu bada tsaraba Suma
To yanxu bamu fito da kudi ba
Ki tambaya nawa ne sai gobe muxo mu siya
Ohk kawai tace ta fita
Ta tambaya tana juyowa kenan ta hango Motocin sojoji suna layi daga dayan bangare want titi
Su Minal baxasu I ganin su ba
Tsayawa tayi tana kallon inda Motocin xasu
Cikin ranta tace kila ma wannan nee Marshal din
Bata gama tunani ba sai taga an bude Masa kofa ya fito
Taku Daya taga ana binshi abaya
Bata da wani nisa dashi don haka tafara tafiya tana son zuwa wajansu
Cen Kuma taga suna Mata nisa
Dabara ta fado Mata
Kawai tayi ihu
Daddy da karfinta
Tsayawa yayi cak Jin Kiran
Dukda yasan badashi akeba
Yace da escort dinsa
Bakuji anyi Kira ba
Zata sakeyin ihun nee wata mota taxo ta banke ta tuni Naj Tai sama ta fado
Ilham ta fito a mota ganin Naj ta Dade waigawan da xatayi taga mota tayi sama da Naj
Ihu tayi sannan ta Kira Minal
Suka nufi wajan da gudu
Jini nee keta xuba
Suka dauke ta sai asibiti
**********
DielaIbrahim ✍️
Vote and Share
Please
YOU ARE READING
BETWEEN US ✔
Документальная прозаStory of three sisters that made alot of painful sacrifices to each other Najmah who happens to be the star of the story, Minal ( Najmah's partner) And Ilham the honest friend
