Chapter Ten

871 77 4
                                    

🎗🎗🎗🎗🎗





               IGIYAR RAYUWA😭




                                          🎗🎗🎗🎗🎗🎗

Story and written by: fateemah Muhammad gurin

Wattpad:- Gureenjo6763

           'Yar mutan Adamawa

Page➡️1️⃣9️⃣▶️2️⃣0️⃣
🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗

Ihun da na sandara shi ya janyo hankalin umaru da ya idar da sallahn magrib kenan yana shirin kora shanukanshi da na mahaifinshi zuwa gida, da sauri yayo inda muke yana isowa ba tare da wata wata ba ya saukewa bawuro sandan goran hannunshi a kai a take ya sheme, duk da sarai ya gane wanshi ne a kaina ba tare da wani tunani ba shima ya sauke mishi a take ya baje shima.................

Da sauri ya kama hannuna ya d'aga ni tsaye tare da d'aukan kwaryan nono na fito me daad'i yayi wa shanukanshi a take suka iso inda muke, duka muka nufi cikin gari, tunda muka fara tafiya nake kuka kaman raina ze fita, yanzu su habu baza su tausayawa maraici na ba? Sannan hamma bawuro kaman ba d'an uwa na ba!! Shine wai ze rako a lalatamin rayuwa..............

Tsoro sossai ya kamani tunda na san ko na fad'awa ummi ba yarda zatayi ba, kuma baze hana gobe ta kara d'auramin tallah ba, gashi ba.... "Ke!! Da Allah ki rufewa mutane baki, akwai wadda ya aike ki ne? In ba rashin hankali ba kina mace me ze kawo ki cikin dajin nan da irin wannan lokaci?".................

Kafin na bashi amsa naji wani abu me tsananin zafi ya ciji kafana ihu na sandara tare da zamewa na zauna a kasan da sauri ya haska torchin da ke hannunshi se yaga katuwar kunama ce da sauri ya take ta, tare da dukawa a lokaci d'aya ya zame d'ankwalin kaina tulin gashin kaina ya bayyana, yaga d'ankwalin biyu yayi inda ya kama kafan ya d'aure da karfi................

Cikin azama ya fara dube dube yana haske hasken torchi har ya samu ganyen da yake nema, ni kam se kuka nake da duwatsu biyu ya samu ya markad'e ganyen tare da sawa a daidai inda kunaman ya sareni, kara na sake Ina me rike hannayenshi a hankali yace "sannu" kai kawai na gyad'a ruwan hannunshi ya mika min na kafa bakin goran a bakina ban sauke ba seda na shanye wasu hawayen na gangaromin.................

"Lallaba ki tashi mu shiga cikin gari dare na yi kar hankalin iyayenki ya tsahi" a sanyaye nace "ko da zan kwna a dajin nan banda wadda hankalinshi ze tashi saboda ni.." da mamaki yake kallo na a hankali yace "sbd me??" Haka kawai naji na fara bashi labarin rayuwana daga farko har kawo yau, na kara da "har yanzu kana ganin laifina don na shigo cikin daji da dare??" Na karasa Ina me kallon cikin kwayar idonshi da suka chanza kala sbd tausayi..............

Da sauri ya kauda kanshi yana me runtse ido ba tare da yace komai ba ya kama hannuna muka mike ba wani nisa ne tsakaninmu da cikin gari ba don haka nan da nan muka isa, har kofan gida ya rakani tare da mikamin kwarya na se da ya ga shiga na tukun ya juya ya fice..............

Ba wani fargaba na shiga don na san ko damuwa da abinda yasa nayi dare ummi bazatayi ba, ai ko hakan ta kasance Ina mika mata kwarya da kud'inta ta soke a zaninta ba sannu bare na gode ba me yasa kikayi dare haka? A sanyaye na wuce d'akina Ina kallon wuyan rigana dake a yage.................

Tabbas da mamana na nan na san cikin tashin hankali zata rikeni tace me ya samu rigana ya yage haka? Me yasa nayi dare a waje? In ban sayar ba bazan dawo tun ido na ganin ido ba? Wani matsanancin kuka ne ya kwace min, kwanciya nayi akan er taburman kaba na Ina rerawa a haka bacci ya d'auke ni dukda tsananin yunwan da nake ji..............

IGIYAR RAYUWA 🎗🎗Where stories live. Discover now