Chapter 17

790 78 1
                                    

🎗🎗🎗🎗🎗





                    IGIYAR RAYUWA😭




                                         🎗🎗🎗🎗🎗🎗

Story and written by: fateemah Muhammad Gurin

Wattpad:- Gureenjo

                  'Yar mutan Adamawa

*An kar'bo daga Aisha tace : madallah da mataye matayen madina, waenda kunya bata hanasu da suyi tambaya game da addininsu kuma su fahimta a cikinshi. Abu dawood ne ya rawaito*

Page➡️3️⃣2️⃣▶️3️⃣3️⃣
🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗

Washegari

Da wuri khairi ta tashi, tayi duk wani aikinta ta gama inda ta musu d'umamen tuwon jiya bayan sunyi wanka sun shirya suka zauna karyawa, su nabeel ma yau zasu fara zuwa islamiya sun shirya cikin uniform d'insu milk da brown sunyi kyau sossai, bayan sun gama karyawa khairi ta dubi dada tace "dada in ban dawo da wuri ba ko ya zakuyi da abincin rana?"...............

Murmushi dada tayi tare da cewa "karki damu kekam ba akwai sauran d'umamen nan a kula ba ki ajiyeshi kusa kawai, in su nabeela sun dawo zata d'uma mana ko kin manta ta iya hura wuta? Ni kuma se in dinga fad'a mata abinda zatayi" murmushi khairi tayi tana zura khimar d'inta tace "Toh shikenan mu mun wuce, zan tafi da su nabeela don ganin islamiyar tasu".....................

Adu'ar sa'a dadan tayi musu da fatan dacewa, suka fice se murna su nabeel ke yi, suna fita gidan Maman hamdeeya sukayi wa tsinke inda a get suka gamu da mijinta suka gaisa cikin mutunci ya fice, a shirye suka same ta so ko zama basuyi ba suka fito da kafa sukayi tattaki zuwa islamiyar su nabeel d'in inda a gaban khairi Maman hamdeeya ta cike komai har en littatafan da ba za'a rasa ba ta saya musu dama tun gida ta saya musu jaka me ABCD din nan da 20leaves kowa d'ai d'ai da pencil.............

Bayan an musu interview aka turasu aji biyu don yaran yara ne masu tsantsan ilimin addini don sossai malaman suka yaba da background d'insu, Asabar da lahadi zasu dinga zuwa daga 7 zuwa 12, yayinda sauran ranakun makaranta kuma 2 zuwa 5. Cikin kwanciyar hankali khairi tayiwa Maman hamdeeya sallama inda ta tari adaidaita ta shige tana ce mishi "Arabian estate"..................

Tafiyar minti goma shabiyar ya isar dasu unguwan, unguwa ne me kyau don yayiwa khairi kyau duk ginin iri d'aya ne se roof dinne suka banbanta layi d'aya red yayinda d'ayan layin ya kasance blue shiru wurin kaman anyi ruwa an d'auke ba kowa, "d'ari da hamsin" me napep din yace da kyar ta samu ya kar'bi d'ari tana mamakin tsadar kud'in napep na gombe..............

Gashi bata iya hawa machine ba ta san da ya fi sauki amma tunda akayi wani gomna na taraba, ya hana machine a cikin jalingo shekaru dayawa bata kara hawa machine ba. She's so curios ta rasa ta Ina zata fara, seda ta shafe kusan mintuna 20 a tsaye kan ta yi shahada ta nufi house no 1, knocking tayi ta jima tsaye kan wata ta zo ta bud'e mata sanye da riga daban zani daban hannunta rike da mopper kallon sama da kasa tayiwa khairi kan ta ce "lafiya" ba tare da ta amsa gaisuwan da khairin tayi matan ba.................

A sanyaye khairi tace "dama aikatau nake nema Dan Allah ko shara da wanke wanke ne a taimaka min" harara matar ta zabga mata duk da itama er aikince amma hali irin na d'an Adam se cewa tayi "bamu bukata akai gaba" tare da rufe kofan da karfi, ajiyar zuciya khairi ta sauke kan ta wuce gida na biyu nan ma wata buduruwace ta bud'e mata amma daga ganin ta er gayu ce itama a yatsine ta amsawa khairi da basa bukata tare da rufe kofan...............

A haka khairi ta dinga bi gida gida har kusan azahar amma bata samu Ko kallon arziki ba, ga kishirwa tana ji, tsayuwarta a kofan wani gida yayi daidai da kiran sallahn da aka kwad'a daga Chan bayan estate d'in a hankali tayi knocking wani matashin saurayi ne ya bud'e mata kyakyawa sanye da shorts da vest kau da Kai khairi tayi kan ta gaishe shi, yadda yake kallonta har ya so ya razana ta a shakiyance yace bayan ta gama gaya mishi bukatanta.................

IGIYAR RAYUWA 🎗🎗Where stories live. Discover now