Chapter fifthy

969 72 1
                                    

🎗🎗🎗🎗🎗



                IGIYAR RAYUWA😭



                                               🎗🎗🎗🎗🎗

💫ANNUR WRITERS ASSOCIATION
(Home of peace, honor, charity and super writers)

Story and written by: fateemah Muhammad Gurin

Wattpad:- Gureenjo6763

                 'Yar mutan Adamawa

Page➡️9️⃣6️⃣▶️9️⃣7️⃣
🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗

Da sassarfa ya karasa ya fad'a jikinta yana jin kewan mahaifiyarshi na dawo mishi sabo hawayen tausayin kansu ya ci gaba da sulala daga idanunshi, mutuwar tsaye dada tayi na mintuna abunda bata ta'ba mafarki ba, bata ta'ba sa rai ba, ko a kiyasce bata ta'ba kiyasta ganinshi yanzu ba sede ba'a mamaki da ikon Allah, Allah aka ce yafi gaban komai yau gashi bata mutu ba Allah ya had'a ta da d'anta da ta fidda ran ganinshi kuka ta fashe dashi tana tuna rayuwansu na baya.

Khairi da tayi narai narai da ido alamun itama kukan zatayi suka had'a idanu da musharraf harara ya sakar mata hakan yasa ta mayar da hawayen nata don dole inna ce ta katse shirun parlorn da cewa "Kai Habu menene wai ka wani tara mutane ba tare da wani jawabi ba kwatsam wani katon saurayi yazo ya fad'a jikin safiya yana ta kuka kaman wadda akayiwa mutuwa" murmushi musharraf yayi yace "Abulkhair kukan ya isa haka plz saketa ka samu wuri ka zauna, inna yanzu zamu miki bayani" sake dada yayi ta zauna shima ya zauna a gefenta tare da riko hannunta se a lokacin yaji kunyan abunda yayin ya kamashi ganin mutane dayawa a parlorn don duk familyn an had'u sbd bukin da suke dashi.

Cikin natsuwa Alhj Abdulrashid yayi musu bayanin kanshi da yadda ya samu Abul inda yana ajiye aya Abul ya d'auka ya musu bayanin bayan fitanshi gida da abunda ya faru dashi inna kuwa ta dinga zagin waenchan mutane yayinda Abba ya sha Adu'a dada ma sossai ta mishi godiya murmushi kawai yayi nan 'yan matan sukayi waje haka hajjiya ruqayya, dada da momma sukayi d'akin dadan inna ma ta tafi d'akinta yayinda haidar da su Jamal suka ja musharraf zuwa part d'in samarin gidan.

Drinks aka kawo wa iyaye mazan inda shafin hira ya bud'e anan Alhj Abdulrashid ya amayar da abunda ke ranshi don d'an boko ne tsantsa be iya rufa rufa ba, sunyi murna sossai inda suka ce zasu tuntu'bi dada, a bangaren musharraf kuwa suna de zaune da su jamal se hiransu sukeyi amma shi kam be sa musu baki ba sam sede abun dariya yayi murmushi, haka 'yan matan da suka kasance su goma sha d'aya chas a zaune a parlorn mommy suna shan hira amare da Adda fadeelah suna site d'in umma little ita kad'ai zaune a parlor tana kallo sbd su nabeel suna makaranta haka Ameer ma, a gaba suka saka khairi da su Amrah suna rokonsu su dawo gidan nan da zama har a gama buki, murmushi kawai khairi takeyi tana ayyana yadda zata iya rabuwa da musharraf na sati guda ta san shima ba yadda ze yi ba sun riga da sunyi shakuwar da ko kwana d'aya da kyar zasuyi In ba sa tare da juna.

Amrah ce ta dubi su Asiya tace "tab ku gama 'bata nyau bakinku kuyi shiru don wannan Juliet d'in baza ta iya rabuwa da romeo d'inta ko na awanni biyar ba bare kwana bakwai" harara khairi ta sakarwa Amrah yayinda 'yan matan suka kwashe da dariya tana murmushi tace "seriously baby baze yarda nayi kwanakin nan ba tare da shi ba amma ku gwada tambayarshi wala alla ya yarda".

Hafsat tace "kaji 'yar air kema kin san ba yarda zeyi ba shine zaki turamu ya dizga mu" Asma'u tace "bare ma yadda yake wani ciccin magani yake 'bata ran nan Ina muka ga fuskan tambaya" Afreen tace "bari zan gwada tambayarshi" murmushi kawai khairi tayi tana girgiza kai kan wayanta ta maida hankali ganin yana haske sakon musharraf ta gani inda ya turo "You are everything I think about. Yes, I am mad. I am madly in love with you." Murmushi me kyau ta saki tana girgiza kai ta fara replying.

IGIYAR RAYUWA 🎗🎗Where stories live. Discover now