Chapter thirteen

808 76 1
                                    

🎗🎗🎗🎗🎗




                  IGIYAR RAYUWA😭




                                            🎗🎗🎗🎗🎗

Story and written by: fateemah Muhammad Gurin

Wattpad:- Gureenjo

             'Yar mutan Adamawa

Page➡️2️⃣4️⃣▶️2️⃣5️⃣
🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗

Three days later

Sossai suka susuce damuwa yayi musu tsananin yawa a cikin kwana ukun nan, har gwara ace mutuwa Abul yayi da irin wannan 'batan shiru shiru sun yi zaman jira har sun gaji sun yi kuka sossai suna kuma kai wa Allah kukansu, a kwana na biyu da 'batanshi khairi ta samu ta lalla'ba Dada inda da kyar ta barta ta tafi police station tayi musu bayani amma se suka nemi raina mata wayau bayan kud'in da ta basu................

A zuciye ta dawo gida tana takaicin banzan hali irin na wasu daga cikin forces na nigeria, a kwana ukun da sukayin nan suna rayuwa ne a matukar takure ba abinda suka saya na anfanin gida kullum sede ta fita ta saya musu abinci shima ba wani na kirki ba, inda sukayi sa'a sun sami makwabciya me matukar mutunci da karamci maman hamdeeya, ta shigo musu sau biyu ta kuma turo musu abinci sau uku ganin yanayin rayuwansu..............

Duk da ba sanin su tayi ba, amma halin rayuwansu yana bata tausayi duk shiganta sau biyun nan samunsu cikin wani hali take, nabeel da nabeela duk sun zama wani iri kaman ba su ba masu wasa da dariya amma sun koma shiru shiru...........

**
Ta bangaren Musharraf kuwa ya ci gaba da rayuwanshi yadda ya saba na kad'aici da shan taba da ya zama mishi aboki kuma kawa da ya ji yana shiga damuwa in ya tuna rayuwanshi na baya se ya zauna ya d'irki na d'irka In ya gaji kuma se ya mike yakai kukanshi ga Allah..........

****
Yau ma kaman kullum zaman shirunsu suke ko taburma ba su da se kayansu da suke shimfid'awa su zauna ko shara gidan be ta'ba gani ba sbd ba tsintsiya, guga da sukaji ana sayarwa a unguwan suka saya se wani bokitin da ta aro musu wurin maman hamdeeya da shi suke wanka suyi alwala da guga...............

Ajiyar zuciya khairi ta sauke tare da kallon Dada tace "dada zaman da mukeyin nan ba shine mafita ba, kud'in da muke kashewan nan tafiya suke ba wadda ke shigowa In har kud'in nan suka kare a haka Toh ba karamin tashin hankali zamu shiga ba, adu'a zamu ci gaba da yiwa d'an uwa, in shaa Allahu baze fad'o kasa banza ba"....................

Ajiyar zuciya Dada ta sauke kan ta fara magana "na san hakan khairi kin rigani furtawa ne kawai ni ce ya kamata in karfafa muku gwiwa a matsayi na na mahaifiya kuma babba amma na sawa kaina damuwa wadda ya shafi har ku, ni uwa ce na fi jin zafin 'batan Abulkhairi akan rasuwar mahaifinku, ban san wani hali yake ciki ba, ban san wani rayuwa ze fad'a ba, yana raye ko mace Allah shine kawai masani" hawaye ta share kan ta ci gaba...............

"Ki shiga gidan maman hamdeeya ki roke ta ko Allah ze sa ta raka ki kasuwa ki sayomana abinda ya kamata se kuma muga sauran chanjin ko Ze ishemu Sana'a" da "toh" khairi ta amsa kan ta mike ta shige d'aki ta d'auko hijab d'inta a natse ta fice tana kallon su nabeel da suke kwance gefen Dada abin tausayi, da sallama ta shiga gidan, wata chocolate color mata ce ta amsa mata wacce na tabbatar itace maman hamdeeya sbd d'umbin fara'a..................

Da ta tari khairi dashi cikin tsokana tace "nayi fushi se yau zanga idanunki?" Murmushi khairi tayi tukun tace "afuwan maman hamdeeya ba gashi na shigo ba, Ina er fara?" Ta karasa tana dube dube "yanzu suka fita da dadynta zasu gidan kakanninta, ki karasa parlor mana bari In gama shanyan nan gani nan zuwa" cewar maman hamdeeyan, murmushi khairi ta saki kan ta nufi parlorn maman hamdeeyan..................

IGIYAR RAYUWA 🎗🎗Where stories live. Discover now