🎗🎗🎗🎗🎗
IGIYAR RAYUWA😭
🎗🎗🎗🎗🎗
Story and written by: fateemah Muhammad Gurin
Wattpad:- Gureenjo
'Yar mutan Adamawa
Page➡️2️⃣6️⃣▶️2️⃣7️⃣
🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗Wayan ya jima sakale a kunnenshi bayan ta kashe kan ya sabule ta a hankali ta fad'i kan katifan gadon da yake kai ba tare da ya bud'e idonshi dake lumshe ba ya dafe kanshi da hannunshi, cikin tsananin tashin hankali yake murza goshinshi da hannunshi dake kai.............
Aure fah Aure kuma? Yanzu? Daga muryan momma ya fahimci wannan karon da gaske takeyi, gaskiya be shirya ba, ya gama aure, ya rufe babin mace a rayuwanshi ya gama yarda da mata a duniyan nan, hawaye ne ya cika idanunshi, a fili yace "Surayyah baki min adalci ba, bakiyiwa kanki adalci ba, Allah ya Allah" gam ya runtse idonshi yana kokarin hana hawayen idonshi gangarowa.................
Hannunshi ya mika bedside drawer ya janyo kwalin Aspen tare da liter ya kunna ya fara sha ba ji ba gani, yana tuna masu sonshin maryam, salima, zainab, Afreen. Shi duk cikinsu ba wacce tayi mishi dabiunsu duk na en boko ne ba na kad'an kad'an ba ze iya rantsewa ko za'a shakuresu baza su ta'ba karanta maka fiye da izu biyu na qur'ani ba da ka ko da qur'anin, Lallai yana cikin tsaka mai wuya................
****
Washegari da sassafe khairi ta tashi dama akwai sauran tuwon jiya da miya, dumame tayi musu me daadi tana saukewa ta d'aura ruwan wanka ta fito ta fara shara tana gamawa ta juye ruwan ta taso nabeel da nabeela tayi musu wanka kan tayi nata ta kuma surkawa Dada ta kai mata, seda ta taimaka mata ta shiga tukun ta dawo ta shirya cikin wani atampha ganta/maso da shima yaji jiki ja da green d'inkin riga da skirt seda hawaye ya zubo mata tuna wadda ya mata d'inkin (Abulkhairi)................
Ta d'aura d'ankwalin a kanta lokacin har su nabeel sun shirya cikin kod'add'iyar shaddansu iri d'aya, abinci ta shigo musu da shi tare da ajiye roban yaji a gefen nata da na Dada don dukkansu masu son yaji ne, su nabeel sun jima da fara cin abinci kan Dada ta fito ita ma atampha marar tsadar kudi ta saka riga da zani be wani kod'e sossai ba zama tayi, suka fara cin abinci da bismillah suna gamawa bayan sun wanke hannu sun shaa ruwa khairi ta dubi Dada tace.....................
"Dada Ina ga ya kamata mu koma makaranta, su nabeela kam ma boko da islamiyya ya kamata mu mayar da su" ajiyar zuciya Dada ta sauke tace "toh khairi In kin je kin sayo abinda ya sawwaka na sana'a In kud'in ya saura se mu duba maakarantun a cikin unguwan nan don bana so kuyi nisa".................
Murmushi khairi tayi cikin jin daadi tace "ze yi ma Dada makarantun gomnati ba a Biyan wasu abin kirki haka islamiyya ma be wuce kud'in laraba ba" Kai Dada ta gyad'a tsam khairi ta mike ta d'auki roba hijab d'inta red color ta sanya tare da zura roba silifas d'inta tana duban Dada tace "na tafi kasuwan Dada" dada tace "zaki gane ko? In fa baki gane ba ki dawo fah" Kai khairi ta gyad'a se kace dada na kallonta, ta fice Dada na binta da adu'ar tsari.....................
A natse take tafiya har ta samu napep ta tsare ta hau ya kaita har bakin kasuwa ya ajiye, 200 ta mika mishi ya zaro chanji ya bata se bata had'a cikin kud'in hannunta ba ta soke shi cikin d'ankwalinta don ta san halinta In chanji sukayi yawa a hannunta zubewa suke, straight ta nufi layin masu sayar da abubuwan da ta zo saya don bata manta ba, ita da wuya tazo wuri sau d'aya ta manta...................
Taje ta saya kuka, daddawa, da kubewa duk na 2/200 ta d'ago hannunta tana zarar masa kenan taji an wabce kud'in gabad'aya tare da artawa a guje, ido ta zaro waje tare da bin bayan saurayin tana ihun a taimaketa kud'inta duk cikin masu sayar da abu a layin ba wadda ya motsa don sun san in ana irin wannan abun kace zakayi taimako kaima yasheka za'ayi.........................
![](https://img.wattpad.com/cover/229264706-288-k522983.jpg)