Chapter thirty three

928 77 0
                                    

🎗🎗🎗🎗🎗





IGIYAR RAYUWA😭





🎗🎗🎗🎗🎗

Story and written by: fateemah Muhammad Gurin

Wattpad:- Gureenjo

'Yar mutan Adamawa

Page➡️6️⃣3️⃣▶️6️⃣4️⃣
🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗

Bata kara kallon inda yake ba ta ja su d'akinta suna ci gaba mata da surutu, harhad'a komai nasu takeyi cikin sauri don kar magrib ya musu a waje bayan ta gama suka fito zuwa parlorn ba kowa hakan yasa ta ja su zuwa d'akin momma sallama sukayi mata ta kira driver akan khairi na fitowa ya kaisu gida, bayan sun fito ta shiga d'akin su Amrah ta musu sallama haka ma nuriyyah..................

Suna fita bayan sun shiga mota little ta sa kuka da mamaki khairi ke kallonta kan ta bud'e ta fito ta duka a kusa da ita tace "little pretty me yasa kike kuka haka?" Tana tura baki tace "I want to go with yhu plzz" khairi tace "sorry pretty ki zauna a gida kinji, ai gobe ma zan zo" tana kallonsu nabeela da suma sukayi raurau da ido tace "but ai bada su zaki zo ba" ba lallashin da khairi bata yiwa little ba amma tace ita kam se ta bi su..................

Tunda suka fara yana tsaye jikin windown parlornshi yana kallonsu yana murmushi da be san dalili ba, ganin taki hakura ne yasa ya had'e rai tare da fitowa ya tsaya a bakin kofa ya ce "little" juyawa tayi tana kallonshi kan ta fara tafiya zuwa wurinshi hannunta ya kama ba tare da yacewa khairi komai ba ya juya suka shige part d'inshi, ajiyar zuciya ta sauke kan ta shiga mota suka wuce......................

Suna isa gida ana kiran magrib, hakan yasa sukayi alwala kawai kan suka shige d'aki sbd hadarin da ya had'e sama ga kuma sauro, bayan sunyi sallahn magrib dada tace "khairi Maman hamdiyya na nemanki tace dan Allah In kin dawo In ce ki shiga" mikewa khairi tayi tana tunanin ko lafiya? Ba tare da ta tsaya karatun bayan magrib ba tace "bari inje inji menene dada" da Toh dada ta amsa ta kan ta fice....................

Da sallama ta shiga gidan Maman hamdeeya dake tattare tattare tana murmushi tace "ke wallahi khairi kirkinki yayi yawa tun yaushe rabon da ki shigo gidan nan?" Khairi tace "afuwan Maman hamdeeya wallahi abubuwa ne suka had'e min gashi ba lokaci ba gashi na shigo ba" Maman hamdeeya tace "dama ke kullum akan bada hakuri kike daga kinyi laifi" murmushi kawai tayi a lokacin Maman hamdeeya ta gama tattare abunda ya sawwa ka tayi mata iso zuwa d'akinta...................

Bayan sun zauna ta matsa ta kama hannunta tace "Alfarma muke roko a wurinki khairi, Dan Allah kiyi hakuri ki amince da bukatarmu na auren baban hamdeeya" da sauri khairi ta zame hannunta tana mata wani kallo na baki da lafiya kan tace "Maman hamdeeya??? Wani irin magana ne wannan anya kuwa kina cikin hankalinki?" Maman hamdeeya na murmushi tace "Lafiya ta kalau khairi kawai de ina son hakan ne don haka ya bukata sannan ni wallahi er uwa na d'aukeki ki amince da auren nan yadda zamu cigaba da rayuwa tare cikin kwanciyar hankali" khairi ta had'e rai kan tace "bana sonshi" Maman hamdeeya ta waro ido tana cewa "ba kunya khairi a gabana kike cewa baki son mijina?".....................

Khairi tace "Au Ashe da kunya, shi be ji kunyar sanar dake yana so na ba? Abarma wannan maganan plz ni na samu wadda nake so yake sona aurenmu kawai nake jira" bata jira amsan Maman hamdeeya ba ta mike ta fito tana kiranta amma ko waiwayowa batayi ba ta tafi bayan ta koma gida ta d'an ta'ba karatu kad'an se kuma aka kira isha mikewa sukayi suka gabatar kan khairi ta saka musu abinci suka ci.....................

Bayan sun gama su nabeel sun kwanta khairi tace "Dada Ina da muhimmiyar magana dake" Dada tace "Ina jinki khairi" khairi tace "Dada........ na samu wadda nake so ne, and kuma yace ba maganar 'bata lokaci yana so ayi aure cikin lokaci kankani" Dada kallon setin da muryan khairi ke fitowa baki sake tayi a hankali tace "aure? Khairi kin san kuwa me kike cewa?" Khairi tace "na sani momma, yana sona haka mahaifiyarshi na sona, haka en uwanshi kinga ba dalilin kin yin auren, In fa kin amince kenan, amma kan amincewarki Ina so in baki labarin waennan ahali inda zaki yanke hukunci ko In shiga cikinsu ko kar na shiga" Shiru d'akin ya d'auka se muryan khairi da ke fita cikin kuka da tausayawa don In itane kam Allah ta tuba baza ta iya jurewa ba, da kullum tana cikin kuka sbd ba karya Allah ya jarabce su....................

IGIYAR RAYUWA 🎗🎗Where stories live. Discover now