Chapter 36

66 11 1
                                    

"kamar yadda kuka sani mahaifiyarku itama yar jahar zamfarace amma ba kauran namodaba wani garine mai suna kasuwar daji, da fari garin kasuwace kawai babu gidaje ba gari a kusa sai daga baya yan kasuwar suka fara tarewa a kusa da kasuwar har wajen ya zama gari wannan yasa ba karamar kasuwa suke da itaba, ina zuwa cin kasuwar garin sosai anan na hadu da mahaifiyarku ita kuma tana kawo talla, a hankali soyayya ta fara shiga tsakaninmu ranar kasuwa ko banyi niyyar zuwaba ko bani da abinda zan kai kasuwar sai naje kawai saboda na hadu da ita, ba dan karamin so nake mataba itama haka, lokacin da na shigar da maganar aurenmu gidansu sai iyayenta suka ki yadda dani suka nuna basa sona ba kuma zasu bani 'yarsuba wani daban zasu bawa"
"munsha wahala sosai dagani har ita kafin mahaifanta su yadda shima ba don sunasoba sai dan ta tubure taki yadda da wanda sukeson su aura mata wannan dalili yasa lokacin da ta mutu basu kara waiwayarkuba fushin da sukeyi dani ya shafeku.

Bayan anyi aurenmu ta tare sai dai tunda ta tare take tare da bakin cikin jaru saboda ban sanar da jaru maganar aurenba sai ranar da za'a kawo kubra, jaru taji haushi sosai kuma dama ta kasance macece mai tsananin kishi dalilinma da na kasa gaya matan kenan da wuri, zamanmu ya zama irin zaman da ake kira da zaman doya da manja kullum jaru tana cikin bin hanyoyin da zata takura ta kuma tsangwami kubra ita kuma kubra kullum tana cikin bin hanyoyin da zata kaucewa shiga harkar jaru idan ta biyota har tata hanyar kuma sai tayi hakuri dan idan har ba a gabana jaru ta yiwa kubra abu ba bazata taba gayaminba, kubra wata irin yarinyace mai tsananin hakuri, tunda tazo gidana sai ya zamana yan uwanta sun watsar da ita ko gidan basa son zuwa wannan ya bawa jaru damar yi mata duk abinda takeso dan tana tunanin bata da gata, lokacin da kubra ta samu cikinku ba karamin bakin ciki jaru tayiba alhalin a lokacin ma yayanta uku sale mudi da salama sannan tana da wani cikin na habu amma bakin cikinta kawai cikin jikin kubra, nasan jaru tayi abubuwa da yawa dan kawai taga bayan cikin jikin kubra amma da yake Allah ya kaddara sai kunzo duniya haka aka haifeku bayan itama jaru ta haifi habu da sati uku, tunda aka haifeku na dau son duniya na dora akanku duk da ina da wasu 'yayan amma ku na dabanne a wajena nasan duk bakin cikin jaru hadda laifina na nuna muku mafificiyar soyayya da nayi, lokacin da kuka fara tafiya kullum muna tare musamman ma dai kai Abdulrahim Abdulrahman dan innarsane dama dan akwai wani lokaci da nake cewa kubra halinsu daya da atbdulrahman sanyine dasu da hakuri ko magana ba damunsu tayiba kuma yafi sonta yafi makale mata ni kuma da Abdulrahim dukkanmu muna da zuciya da kuma surutu shiyasa ma idan munyi zuciyar muke saukowa da wuri, tun daga kanku sai haihuwa ta yiwa kubra walaha bata kuma haihuwaba idan ta samu cikin sai ya zube tana damuwa sosai akan hakan haka zan zauna nayi ta bata baki har Allah ya kawo cikin Khadija lokacin shekarunku takwas ban san abinda ya faruba nasan dai kubra ta sanarmin tana da ciki nayi ta murna ina adduar Allah yasa me zamane na fara karbo mata magunguna wajen wani mai magani da kuma rubutu wajen wani malami tana sha wata rana ma har takeyimin maganar ya kamata na barta wannan karon taje awo saboda yadda kullum ake fadakarwa akan zuwa awo a radio ita kuma ma'abociyar jin radio ce sosai, a lokacin na yadda zan barta amma kawai daga kwanciya barci wata la'asar ina tashi naji babu abinda na tsana kamar kubra, da na kalleta sai naji wani irin haushinta ya kamani, saboda haka kuma na daina shiga harkarku kwata-kwata na daina kulaku kullum sai dai fada da hantara har da duka ranar da ta tunamin maganar zuwa asibiti awo kuwa har marinta nayi nace ga jaru nan duk haihuwar da takeyi bata taba zuwa wani asibitiba sai ita zatace zataje na kare mata zagi tas, dan kiwon da takeyi da yake babarta ta aiko mata da kiwonta tana kiwo dashi haka nayi ta dauka ina sayarwa ba tare da neman yardartaba idan tayi magana na kare mata cin mutunci, zan iya tunawa akwai lokuta da dama da jaruce zatace min tana bukatar kudi idan nace bani dashi sai tace na ari kiwon kubra mana haka zanje na dauka kamar wanda uwarsa ta sakashi ba tunani ba shawara bana kuma iyayin musu daga baya idan na fara mitar inason na maida mata abinda na dauka sai jaru tace ai basai na mayarba da kai da kaya duka mallakar wuyane akwai lokacin ma danace ni kam sai na maida sai cewa tayi ai dama dazu taji kubran na baku labari tana cewa wai duk dabbobin da nake dauka bata yafeba kuma ko ta halin kaka sai na biyata dukiyarta wai taji kubran tana ta zagina kuma kuna tayata shiyasa tace kar na mayar dan idan na mayar zaku rainani kuce abinda ta fada ya tabbata ta saka dole na dawo mata da dukiyarta kamar yadda ta fada, a lokacin raina ya baci sosai naje har daki na karewa kubra zagi baiwar Allah tana kuka tana kokarin tayimin bayani ko kuma ni na gaya mata laifin da tayimin amma naki sauraronta nayi ficewata bayan na gama wulakantata"

ALMAJIRI MA 'DA NE (Editing)Donde viven las historias. Descúbrelo ahora