*SILAR GIDAN AIKI*
NA
*UⓂMIEY XEEY**Wattpad@Freshummieyxeey*
*NOTE🚫* _Masu tambayan account number ko Wani number da za a turomun Card, Kusha kuruminku NOVEL dinnan is *FREE🤩* nayine dominku FANS Dina....All I want from you is DU'A Allah ya biyama kowa bukatunsa na Alheri_
*PAGE 5⃣*
Both uncle Abdallah and Corper Munsur turaki maida idonsu sukai kofar class din adaidai lokacin itama Nazeefa ta kalle kofar Class din tana tinanin barkatai azuciyarta
Hada ido Nazeefa sukai da Mansur turaki, tsigar jikinshine ya tashi Sosai, nan take yaji wani irin yanayi na shigarsa, labbansane naga suna motsi kamar zai furta wani abun sai kuma yai shuru
"Abdullah yace Yadai?
Girgiza kai yayi Alamar bakomai, Mik'a ma Abdallah hannu yayi sukai Sallama yace" Mai ni na tafi but inshaa Allah zan dinga zuwa muna gaisawa, but bani number wayarka
Nan sukao mosayar number, M.T yace Bye Am going
"Abdallah yace OK badamuwa, Sai najika
Mansur Turaki direct wajen motarshi ya wuce, yana tafiya kamar baze taka kasaba, balle kuma yaji kijinsa yai sanyin bansan daliliba, key yasa ya tada motar
baba megadi yabudemai gate ya fita
Ita kuma nazeefa kamar ance ta kalle bakin gate ta hango motarshi yana Fita, AAransta tace this man yanada tausayi daga gani, kamar ta kwalla ihu takeji, Kome yasa takejin Haka ohon musu, Tsaki taja ahankali
Maganar uncle dinsune ya dawo da ita daga dogon tinanin da takeyi, Kawai ji tayi yace" KO zaki bishine?
"Ta ce Wa?
Yace Wanda kike kallo mana, duka Class din suka kwashe da dariya
Kawai ta sunkuyar dakai aranta tana cewa bakasan halin da nake ciki bane, Meye hadin jirgi da mota hmmm
"Ya gama period dinshi ne zai fita ya kalleta yace" you can go a sit down
Ko kallanshi batai ba Tace thanks
Ya sungumar Yar jakarshi yace" bye class, Sukace have a nice day uncle
Tashi tai ta kakkabe kayanta taje kujera ta zauna, Babbar kawartace da suke zaune a kan kujera daya ta kalleta ta rike hannunta tace" kidena zuwa latti please banaso ana wulakanta ki,
Nazeefa ta kalleta ido cike da kwalla tace" Nafisa amma Kinsan halin da nake ciki Ko?
Yanzuma kafin tahowana bakiga yanda Mubin yamun ba...nan ta kwashe labarin tun dawowarta jiya har safiyar yau
Nafisa Ta cije labe tace shine baki Rama? ai Wallahi da nine sena rama sedai aita mare mare
Nazeefa ta Nunfasa tace" Aje dai zuwa, but bazakigane bane, kawai ya teanenine, Nafisa tace" Sai hakuri amma wasu iyayan basu ma yaransu adalci wallahi, Yanzu zaman gidan wasu sai hakuri, Nazeefa tace" kibari kawai muna ganin rayuwa Kala Kala,
Break nayi sukadan fita Kowa se nuna Nazeefa yake, Daga masu cewa Tana basu tausayi sai masu cewa cewa ai yarinyar ta cika taurin Kai suka Dan kewata a school din suka koma Class Dinsu 12:00PM nayi akai closing
Bakin gate Suka zo suka Tsaya, Yara sai tafiya gida suke, Nafisa tace" kizo muje mana, ko ya Mubin zaizo daukar kine?
Saurin kallonta tayi tace" ya wa? Tace tace" ya mubin Mama
Nazeefa tace" Allah yakauta nacemai ya mubin saboda da ya mubin dinne bazaimun abundayaga dama na
Nazeefa sai jinjina maganar Nafisa take wai ya mubin, tabe baki tayi tace" Saifa ya mubin ai da yazo ya kaini gida AI gwanda na taka a kafa, Nafisa da sauran frnds din sukai dariya dan yanayin da tai maganar ne yabasu dariya
Suna Tafe suna Hira,
Faeez da faeeza ne Suka hango Nazeefa tana tafiya da kawayenta, faeez yace" Ya mubin ga Nazeefa Chan ka tsaya ka dauketa please tunda gida zamuje
Wani harara ya balla mai. Sai a daidai lokacin ya kalle inda Nazeefa take, Moto suka gani yayi parking a gabansu yace" Ina zaku?
Dan mutumin yana tausayin yara sosai, sau tari yabiyo hanya yaga yara baya tafiya saiya ragema Wasu hanya
"Ya ce Ina zaku
"Sukace chan Kasa
"yace to ku shiga Zani masallacin jumma'ah ne ko a tini na ajeyeku
Nazeefa da biyu ta shiga motor dan ta hango Motar mubi, Dan a ranta tace dadai tabi Mubin gwanda ta shiga ko motor waye
Shiga tayi batasan ma waye ba, Kallon mazaunin driver tayi taga uncle *MANSUR TURAKI* ne, Wato har ya je gida yayi kwalliyar jumma'ah lalle kuwa masu abu da abunsu, Tinani ta shigayi sosai, kawarta da sauran kawayenta suna Ma nazeefa tsiya sukace" su Nazee anje AC anyi tsit, Dukansu Suka kwashe da Dariya
Mubin ko dayaga Nazeefa ta shiga motar fitowa yayi ya kalle yarinyar yace" Ahab Ashe abun da yarinyar nan takeyi kenan lalle yau zataci ubanta, Sai huce yakeyi
Shiga motar yayi, yajata Puuuuuu Basu dadeba sai gasu a kofar gidansu
Tun a bakin gate yake ta horn akai sa'a baba megadi yaje Sallah
Dan zafin rai kasa shugowa da motor yayi, Tun a waje ya sauka yake kwalawa hajiyarsu Kira
Hajiya....
Hajiya
Gaba daya hankalinta ya tashi ta fito pallow da Tazo ta ganshi a tsakar gida
Tana My son meya faru, inasu nazeefan dasu twins
Yace hajiya akwai matsala idan yarinyar nan ta dawo Gaskiya ki tarkatata da komai Nata ta koma gida Dan bazataja mana Abun kunya ba
Hajiya tace" banganeba me kkeso kacemun
Idonshine Yai jaaa na mugancine ko na kishi ni bansaniba
Huhhh lemme stop from here
PLEASE FOLLOW ME ON WATTPADD *@freshummieyxeey*
YOU ARE READING
SILAR GIDAN AIKI
Fantasifiction Story.......labarin wata yarinya me suna Nazeefa, ta taso cikin wahala, Tasha gwagwaryar rayuwa.....