*SILAR GIDAN AIKI*
NA
*UⓂMIEY XEEY**Wattpad@Freshummieyxeey*
*PAGE 6⃣3⃣*
*Washe Gari*
Nazeefa Tun safe data tashi take trying number Mansur sedai ace mata Switch off, Hankalinta a tashe yake Dan tasan ba karamin Abu bane Zaisa mutun ya kashe waya, Tinani barkatai take tayi aranta tace kodai beda lafiyane Dan Sam bata kawo wani Abu akan auransubaKira takeyi harta gaji, Gaba daya batada walwala, da yake Mahaiyarta me lura ne sosai ta zo ta sameta tace meke damunki?
Nazeefa tace bakomai, Umma hafsat tace kalleni dakyau Nina haifeki ki fadamun meke damunki? Nan Take Nazeefa ta kirkiro karya tace Mammah Wannnan mutumin ne beda lafiya yau kwananshi 2 ko magana be iyawa
Subhanallah mamanta tace gaskiya dole ki damu, Yaya jikin nashi? Nazeefa tace da Sauki umma, Tace to Allah Kara sauqi Dan Allah kigaishehi, Nazeefa tace Inshaa Allah Umma sanan tabar dakin
Tana fita Nazeefa Duba gallery dinta ta farayi nan taga wani pic na Love of her life yana smiling, kwalla ya xubo mata aranta tace inason wannan guy din!
Kallon pics dinshi sosai tayi sannan tana ta Kira yaqi shiga, Samun waje tayi taci kukanta sosai, ita
Tana ta tambayar kanta kodai tamai wani abune yake punishing dinta,
Text ta turamai kamar haka, _I called ur line several times yaqi shiga Dan Allah idan ma laifi nama kayi hakuri dan na azabtu habibee, ina kaunarka har Abada_ sannan ta tura mai duk bayan minti kadan take duba message din ko yayi delivered idan taga beyiba setai tsaki ta jefar da wayan kan gado ammafa hahahhh
Tana cikin dakin ranar dai ba wani walwala taiba, Ko abincima ta kasa ci, tana tinanintane bacci ya kwasheta
Bayan tai bacci Mahaifinta ne ya dawo, Ya sama Umma a tsakar gida akan tabarma tayi shuru tana zaune
Zama kusa da ita yayi yace lafiya Ina Nazeefa take Naganki ke kadai?Cemai tayi Nazeefa na daki bacci takeyi, kasan ko Wannan Saurayin nata bashi da lafiya?
Yace Allah sarki, Allah ya bashi lafiya amma dai taci abinci KO? Tace Anya kuwa bansaniba Nan suketa hirarsu***
Nazeefa na bacci taji Wayarta Nata Kara sakonnin nata shigowa Dan haka tai zumbur ta tashi
Daukar wayar tayi ta Fara karanta sakonnin da yake ta shugowa, mamaki ne sosai ya kamata aranta tana waye ne wannan me mun kalaman nan,Text din karshe ta ke ta maimaita tawa kamar karatu, "Kisani idan har baki amince na aurekiba to tabbas Zan iya rasa raina, nine nan boyayyar masoyinki, I love you...
Sake sake ta farayi what's happening, Waye wannan kuma, Tsaki tayi ta ajiye wayar taji komai be Mata dadi, ita kam ko waye sedai yai hakuri Dan batada space a zuciyarta Dan Mansur ya riga ya I occupying heart dinta gaba dayaSo ba Wanda zata saurara koda waye kuwa
Tagumi tayi jum, nan tinanin Mansur ya addabeta Dan haka ta dauka wayar ta kirashi still A kashe Salati tayi, Tace Anya ba mutuwa mansur yayi ba, Fitowa Waje tayi ta tarar da mahaifanta tuni ta zube a kasa sumammiya
Salati suka Fara Umma Hafsatu ta ebo ruwa ta yayyafa Mata Ta fargado, daukarta sukai taka kaita daki, Suna tambayarta meya farune? Mansur kawai take ambata
Nan mahaifinta Ya lallasheta yace karta damu, Jibi jibin nan zasu koma suje meke faruwa, Dan haka tai smiling Tace nagode Abba
Umma kuwa ta dakko Mata abincinta taci ta koshi nandai suketa bata hakuri akan komai zaizo da sauqi inshaa Allah
Chan yamma nayi Baban Nazeefa ya Kira Baban mubeen Akan aikin gidanshi, Yace angama dai KO Dan nasan akwai kudi akwai komai da komai!
Baban Mubeen yace angama fenti ne kawai za'ai Dama banfada maka ba akwai wani gidan already angina shi Chan bayan gidana! Shine mukai shawara a gyarashi idan yaso kadawo be maka se cikin filayenka ka zaba se ai maka Wanda kakeso
Bban Nazeefa yace OK Madallah nagode sosai
Suna gama waya ya Kira Mubeen akan yaje chan gidan aikin ya gani, kafin yazo, so yake zuwa gobe agama komai Dan jibi zasu dawo
Mubeen yaji wani sanyi aranshi yace OK Allah takaimu
Daki ya shige Ya dauka wayarshi ya ya Kira line din Nazeefa, Dauka tayi tace Hello, ba ai magana ba ta sake cewa hello, Waye ne?
Wani Murmushi yayi da yaji voice dinta sannan ya kashe
Mubeen yace ahankali zaki dawo da sona ne,
Shiryawa yayi ya tafi Wajen ginin Su Nazeefa yaga komai na tafiya daidai
Se Chan dare ya dawo ya sanar da mahaifinshi yace Masha Allah
Muje Zuwa
FOLLOW
VOTE
COMMENT
YOU ARE READING
SILAR GIDAN AIKI
Fantastikfiction Story.......labarin wata yarinya me suna Nazeefa, ta taso cikin wahala, Tasha gwagwaryar rayuwa.....