ZUCIYAR MASOYI
💖💖💖
💗💗💗💗💗AISHA A BAGUDO
Page 24
Gabadaya faiza tagalabaita tagama fita haiyacinta numfashin ta ma gagaranta yayi " yayin da boka bai ma san wani duniya ke ba ,dan bai da niyar saurara mata, hakar ta kawai yake son ransa ga wasu gumi na kazanta dake fita ajikinsa masu mugun wari, sai da ya tabbarwa kansa ya gamsu iya gamsuwa tukun ya sarara mata ya Mike yakoma gefe daya yana fidda numfashi hade sharce gumi dake tsiyaya a goshin sa ,wanda a dai dai wannan lokacin da numfashin faiza dade da tsaya cak tashi tsaye yayi yana duban inda take kwance yatabe baki yana jijiga kai yace koda ke din ba budarwa bace Amman kinji jiki. sannan ya sake gayara tsayuwarsa " ya dauko dan kanfen shi ya manna a gabansa ya koma gun aikinsa yacigaba da attending customers to haka dai mata suka rinka shigowa suna fita daya ga wacce kallaeta ta dauki hankalinsa zai ce tajirasa yana zuwa kusan awa uku kennan faiza bata farfado ba haka Kuma ko motsa ba tayi ba " batada alamun motsawa har sanda ya sake shigowa dakin yace wannan fa neman take jamin maseefa ina zaman zamana idan ko baki farka ba sunanki sorry " yaje ya debo wasu ruwan magani da aka dade da tsuma sai wani wari wari suke ya watsata, Amman shr kake jin faiza ya dago kwaryar ruwan gabadaya ya juyo mata a kai " take ta sauke ajiye zuciya yacigaba da watsa mata a zuwan wanka maganin yake mata" sai da yagama ta Mike da kyar sannan ya Miko mata kayanta ya fita byn kmr mintina uku sai gata fito tana dingishi ta zauna wani kwababban abu yabata yace a daren yau zaki mulke jikinki da shi duk yadda za ai kibari jikinki ya hadu da na Abdullah din muddin haka ta faru sai dai a daura auren da wani Amman bashi ba dan tun dazu muntara aljani makeetu yana can yana sauran aiki " jiki yana bari faiza ta karfa tana godiya kmr ba ita tagama shan wuya ba" awanin da suka wuce' har zata fita yace ki kula da kyai kar ki shafa da sauran haske sai gari yayi duhu ko Kuma ki aiwatar kafin fitowar alfijir kafin kiran sallar safiya kennan makarin sa hasken rana ne da kyar faiza ta iya mikewa. Tana dingisa kafarta hankali ,dan duk ilahirin jikin ya mata nauyi a haka ta bar cikin kauyen...
Takwas ta wuce Sannan dady ya shigo ya shiga part dinsa Abdullah ya bashi kmr awa daya sannan ya bishi duk akan idon faiza hakan ta faru domin tun dawowarta gab da magariba bataga gilmawarsa ba sai yanzu dama abinda ta yanke idan bata ganshi ba zata bi dare ta kwankwasa masa kofa tasan zai zo ya bude yaga kowaye yana budewa zata rukunkume shi da maganin a jikinta ..
Yayi sallama ya shiga dady yana ganinsa ya fara murmushi" kamar dai kowane dare sanye yake cikin kaya marasa nauyi yana binciken wasu file ,Abdullah ya isa gareshi ya zauna a gefen tuntun dake kusa da shi baza baza dady ya zube file a gabansa har katin daurin auren yana dubawa shr Abdullah byn ya gaishe shi dady ya dago Ido ya kalli yanayin da dan nasa yake Sannan ya dauke kai yacigaba da abinda yake. yace yaya dai Abdullah any problem?
Cikin sanyi jiki da sarkewar murya Abdullah ya sunkuyar da kai ya ma kasa maganar dady yace mhm ina jikinka ?Abdullah yadan kalli dady da rawar murya yace dady mami tadaina kulani yakarashe maganar yana zubda hawaye..... kallon da dady ya masa shi katse shi yasake yin kasa da kanshi yace dan Allah dady in zai zai yiwu a daura auren da duk wacce mami ke so dan idan na aure Aisha mami bazata Kuma kallona ba.. Ido jawur yacigaba dady da gaske mami bata son abun nan cikin inda inda yace ni ...Ni na .hakura kawai dady ya bar abinda yake ya zubawa Abdullah Ido na tsawon lokaci yana nazari akansa sannan yakirawo sunansa yace Abdullah ka kwantar da hankalika kana yawan sa damuwa ya zama over a ranka byn duk abinda doctor yace a kanka ,ya dan yi shr sannan yace Abdullah bbu abunda aka fara shi ba a karasheshi ba duk wani abu da za'a yi a rayuwa to tabbas wata rana zai zo ya wuce yana magana yana kallonsa yace Abdullah yau aka wayi gari bbu Raina kai ne ke da alhakin rike min dukkan iyalina dana bari to sai nakasa yima abunda zai kyautata taka rayuwar .
wacce maminka take son ka aura ko kadan bata dace da rayuwarka da nayi niyyar ka hada su duka ka aura Amman dana sa ayi bincike akan banji dadin abunda akatarar akanta ba , ya numfasa Sannan yace yawancin bata garin zuria idan ka duba ya faro ne daga ainihin maaurata ,Abdullah mace ta gari itace ke sa mutun ya samu natsuwa da kwanciyar hankali da zai zama cikakken mutun mai iya rike gidansa dan haka ka dai na maganar ka fasa aure da yarinyar nan awanni kadan ya rage a daura auren ku muddin kaga baayi ba yin Allah ne bai karasa da numfashin na ba Amman sai anyi Sannan Abdullah na tokeka karike amanar yarinyar nan ba wai dan tana diyata ba, saboda bakasan iya wahalar dana sha ba kafin kasamu aurenta Abdullah ya kada kai yana duban mahaifinsa dady yace Allah yayi muku albarka kai da ita ka rike wannan a ranka itama mamin da kanta wata rana zata sa muku albarka" dan yanzu bata San gatan har da ita akayiwa ba ..jikin Abdullah yayi sanyi sosai dady yace ka cire dumuwa a ranka komai mai wuce wa ne ya dubi agogo tashi kaje ka kwanta dare ya fara gashi za'a tashi da wuri ahankali Abdullah ya Mike cikin sanyi jiki ya juya zai fita har ya kusa fita dady yayi gyaran murya Abdullah ya waigo ya nuna masa hanyar bedroom dinsa yace ka shiga ciki ka kwanta Abdullah ya juyo yana kallonsa sannan a hankali ya dawo yabi hanyar bedroom din dady ya shige sanin dady ne mai yiwuwa idan ya koma part din nasa yacigaba da yawan damuwar shi yasa yace yashiga nasa dakin ya kwanta ..Hummm Su faiza kuwa an tsufa can cikin shuke shuken fulawowi dake daf da kofar da zata shiga da kai part din Abdullah ,duk da damuna ta dan gota Amman har yanzu ciyayi da shuke shuke sunan a korensu haka ne ya taimakawa faiza samun maboya a cikin su a tsugunne take a takure gashi ko kwakkwaran motse batayi saboda kada yaga motse a gurin yaki fitowa ga warin maganin da ta shafa a jikinta duk ya Dame ta har dare ya tsula ba Abdullah bbu alamunsa anan tagane wasu abubuwa sukeyi tare da dady na daurin auren, shi yasha kansu a koda yaushe yana iya fitowa yazo ya kwanta dan haka tacigaba da Jira ga sauro sai cizo suke sun samu nama" jiya tayi kwanan ha'ulai a kofar gidan boka mai gani har hanji gashi yau ma zata sake kwanan gidan sauro. baya da kugunta duk sun rike mata sai da takai ga zaman dirshan a wajen iya tashin hankali faiza ta ganshi agun dan har kwarika suka dinga bin jikinta ga bacci a idonta Amman dan jaraba da kafiyar irin nata ko gezau balle ta bar gun ita dai sai burinta ya cika " har sanda akafara kiraye kirayen sallah a wasu masallatai dake kusa da su tun tana karyata kunneta har taji a masallaci dake cikin gidan duk ilahirin ruwan jikinta ya kusa tsotsewa bata amincewa ranta ba har sanda taga kofar part din dady an bude dady ne da Abdullah suka fito a tare da alamun masallaci zasu je dan ca suka nufa nan duniya mutumin dake cikawa faiza Ido Kuma yake balain yimata kwarjini irin dady. Ban cin haka ai da tunin tayi gudu ta Tari Abdullah a wannan lokacin duk da tasan kaidar da boka ya gaya mata Amman tasan muddin ta doshi Abdullah a wannan lokacin tasan daga ita har mama hafsa kashinsu ya bushe dan sai anyi tambari da gabadayansu anyi sama da su ..
Tun karfe bakwai Dr sagir ya iso gidan, dady ya turo da kayan da Abdullah zai sa hum maikaratu ba sai an tsaya kwatanta tsaruwarsu ba, tun safe kuwa manya manya da kusoshin gwanatin duniya suke cincirindo a gidan har police aka sanya sannan akabar Abdullah ya fito ya shiga motar zuwa gidan alhaji aminu kai daga kallon shigar manya kayan da Abdullah yayi kasan dole ce kawai tasa shi sanya su don hatta leben babbar riga a hannun salis take shi kuwa da kyar yake iya daga dayar ya mai da kan kafadarsa ...
Hummmm ga dai Abdullah zaije gun daurin auren to jama'a ko ya auren zai kasance , to kudai biyo Yar mutan bagudo kusha labari🤝🤝😜😜
MMN SUDAIS CE
YOU ARE READING
zuciyar masoyi
Romancezuciyar masoyi labari ne akan tsantsar tsaftatacciyar soyayya mai had'e da yan'uwantaka, yana matukar kaunarta fiyye da komai nashi, sai dai adaidai gabar da zai mallaketa ,mahaifiyarsa ta kawo wa zuciyarsa da rayuwarsa tsaiko .......