[3/12, 3:01 PM] Kaunace Sila: 💗💗💗💗💗
ZUCIYAR MASOYI
💖💖💖
💗💗💗💗💗AISHA A BAGUDO
Page 41-42
Jikinasa yaji a lokacin ya daina rawa sai babban dan yatsan kafarsa kadai ke motse .
ya dubi takardar gabansa ya dinga kallonta tamkar ma ba takarda ba.
yana jin hayaniyya akansa Amman baya gane abinda ake fada ba.
ya dauki Biro ya daura akan pepper sai ya tsaya shi kwata kwata bai san yadda ake rubuta saki ba .
Mama hafsa da ta fahimci haka tace sawa zakayi kai Abdullah ka saki matarka Aisha saki uku shikenan.
ka huta da jaraba .Minal ce ta fado falon ta tana kallon inda yake zaune kmr gunki.
Byn tagama jin duk abinda su mami ke cewa.
ta tuna da maganar malamin dayake zuwa yana koyar dasu har gida a fannin addini yabata yi musu bayani game da babin aure da saki .
yace Allah da kansa ya halicci saki Amman baya sonsa mafi kysunsa ne ayi saki daya .
dan haka ranta dake mugun bace " ta isa gurinsa tace yaya ance ba kyau a saki macce saki uku .
saki daya ma yaisa dan haka ka rubuta saki daya .Mami ta daka mata wata irin tsawa da frigita gabadayansu, dole ta bar falon .
da yake itace magana ta karshe da minal tai masa dan haka ya rubuta saki daya ya turawa mami takardar kusa da kafarta.
ya dafe goshinsa da kirjinsa lokacin daya ya fita haiyacinsa wani juwa yaki kansa nayi Amman yana nan a gurin bashi da niyar barin gurin .Mami ta dauki pepper ta duba ta Gani tace ko rabin saki kamata nagode balle odindin daya.
Tace kana iya fita .
ta Mike tsaye itama mama hafsa ta karba ta Gani tace an dai rubuta sakin .
yanzu nan za'a kai mata mami tace yanzu kuwa tun dare bai mata ba aje akwana cikin duhu a gidan gyatumi tace eh .Aisha na nan kwance yadda Abdullah yabarta Amman kmr anyi mata duka haka tarinka ji ajikinta da zuciyarta tamkar yadda ta ji a dazu.
ahankali taji karar mota bbu wanda ta bawa ranta sai Abdullanta ne .
ta danyi murmushin ta sake kudindinewa.
wai idan yashigo ya dauka tayi bacci ,.
Amman a yadda ta jiyo ana bude kofar cikin gidan ana shigowa da hargowa tasan bashi bane.
tayi sauri tashi ta zira rigar baccinta yayinda tarinka jiyo maganganu a falo ana hade kiran sunanta.
Yasa ta juya tana duduba gefe da gefenta ta wawuri wani zani da tayi wanka dashi dazu ta daura ta sanyo hijabin sallah ta fito .
Karo na farko kennan da mami ta taba ganinta .
a lokacin mami kmr ma ba a cikin haiyacinta take ba.
saboda tana son taga wacce mayyar yarinya ce ta kama mata ZUCIYAR Abdullah.
kawai taga fitowar AISHA.
ba haka taso ta ganita ba.
Yar yarinya Yar cikinta sai da suka kalli juna ita da mama hafsa .
akwai wani sirri dake jikin suruka da uwar miji wanda dukkansu sai da suka ji shi ajikinsu saboda shi dama namiji adan aka halicce shi daga jikin mahaifiyarsa byn wani lokacin sai ya koma jikin matarsa ..
to wannan sinadarin ma yayi matukar tasiri azuciyar kowanne su dan daga mami har Aishar haka sukaji .Mama hafsa ma kanta saida ta Raina yarinyar tace ,"ho ni hafsa yanzu Abdullah kan wannan abar yake wani hauka da tashin kai .
ko me zai ci ajikin wannan "oho".Mama hafsa Tace kinga ungo wannan kinji.
mijinki ne ya sake ki.
AISHA ta tsaya tana kallonta tana son manna mata hauka ta gane matar tun farko zuwan da suka yi gidansu.
mama hafsa tace karba ki duba mana kin tsaya kina bina da idannu .
idan kinga zaki iya tafiya yanzu to ga hanya nan a bude take idan kuma sai gobe ne ma duk daya.
Dan za'a kulle musu gida mami dake zaune kasa magana tayi.
AISHA tasa hannu ta karba takardar jikinta na rawa.
bata bude ba kmr yadda matar ta umarceta dan tasan haka din ne .
tunda ga mahaifiyar mijinta nan zaune .
Tana tsaye ta rasa abin yi ta sake ce mata ciki zaki shiga ki dauki abinda zaki dauka .
dan nasan kina fita zaki samu bus din zata kai ki wannan banzan lungun naku .
![](https://img.wattpad.com/cover/205938711-288-k658577.jpg)
YOU ARE READING
zuciyar masoyi
Storie d'amorezuciyar masoyi labari ne akan tsantsar tsaftatacciyar soyayya mai had'e da yan'uwantaka, yana matukar kaunarta fiyye da komai nashi, sai dai adaidai gabar da zai mallaketa ,mahaifiyarsa ta kawo wa zuciyarsa da rayuwarsa tsaiko .......