Sha Uku

289 57 1
                                        

Fuskan tan abinda ba ka shirya mai ba karamin rikice ne dashi ba. A kwana biyun nan gabadaya Barr Mustapha ya shiga wani mawuyacin hali. Da dukkan zuciya da karfin guiwan shi ya ke jin son tsaya ma Suhaima. Sai dai, gabadaya ya kasa gane in dai zai fuskanto wa abin. Yayi magana da Faroukh sai dai bai samo wani abin Kirki ba. Yawancin labarin akan abinda ya sani tsakanin Suhaiman da budurwa zayd ne da kuma shi kanshi zayd. Ga fahimtar Faroukh, suhaima na da wani mugun nufi tuntuni akan zayd da ta ke boyewa. Abubuwan dai duk rudani su ka kara mishi, shi da ya ke neman hanyan kare ta gabadaya points in da Faroukh ya bashi is aginst her. Karin karawa yana mamakin a ce wai Suhaima ce ta aika ta wannan abubuwan. Tirkashin fa kenan!

Yau ya ke shirin koma wa Abuja, yana bukatar ganin Suhaiman su cigaba da tattaunawa kan lamarin. Abinci mai rai da lafiya Maryam ta hada mai, yayi farin ciki sosai duk da bai iya sakin jiki ya ci abincin da kyau ba. Hira ta ke mishi jefi jefi tana sako mishi kishin ta "Mu dai kam Suhaima ta dauke mana kai" za ta fada sai kuma ta waske kaman wasa ta ke. Sai dai ba halin mimin nashi da bai sani ba, a yanzu ba wannan bane matsalan domin bai da karfin guiwan yi mata bayani ba, in har ita da kanta ba ta san ya kamata ba.

Buzz buzz, karan wayan shi ya dawo dashi daga tunanin da ya dan fada. New numba ne hakan ya sa shi sharewa sai dai yanda calls ke ta shigowa wayan ya sa shi daukan wayan dole. Sai ya dauka ya ji muryan mace sannan ya kara duba numban da kyau, sai lokacin ya gane numban da suhaima ta bashi ne.

"Hello" yayi saurin fada gudun ta katse wayan.

"Ehmm ina jinkaaa ai,  na ji kayi shiru ne" ciki da duniyan ci ta ke magana, sai dai daga yanayin sautin muryan ta za ka gane hausa bai gama zama a bakin ta da kyau.

"Dan Allah ina magana da Zeenah ne?"

"Zeenah ke magana amma fa in kana bukatan harka ne dole kayi hakuri zuwa ranar Alhamis, bana cikin lagos" shiru yayi yana mamakin rashin kunya a fila irin wannan, sai kuma wani abu ke gaya mishi to daman kana bukatar ganin kunya gun karuwa ne?

"Amma kina ina ne? Dan gsky a matse na ke kuma ke kadai ce na ke ganin za ki iya kore min kishin ruwa ta" ya mata hakan ne don ya samu hadin kai sosai a wurin ta.

Wani shakiyin dariya tayi tace "toh fa, maza a samu labarin mu kenan. Gsky nayi nesa da lagos sosai"

"Kar ki samu wani damuwa ko ina kike dole ne in biyo ki ai" ya amsa ta cike da kosawa wannan karan, burin shi dai yaji garin da ta ke in yaso daganan ya tattauna da Dr sun san yanda za su bullo wa abun.

"Asuban cin bari garin kaduna zan yi zuwa birnin tarayya gobe in Allah ya kaimu" ai bai san sanda ya saki wani ajiyan zuciya ba, jin komai na kokarin zuwa mi shi da sauki.

"Yana ji kayi shiru?" Ta kara fadi, don har ta fara murnar kamun da tayi.

"Ina garin kaduna yanzu haka, ya za ayi mu hadu"

"Kai kai ina tare da wani mugun ne fa, da zai yiwa da mun hadu a Abujan gobe in za ka iya" ta amsa shi tana faman ya amince ds hakan, wanda ta ke tare dashi in bata ganin zai bata damar fita wuri ita kadai.

"Haba yan mata da dai kin taimaka min mun hadu a yau in, na fada a kagauce na ke fa" shiru tayi tana tunani sannan tace "zanyi kokarin fitowa mu hadun amma fa ba za mu dade, dama za kayi hakurin goben ne"

"Kar ki wani damu ba sai kin daden ba in yaso na kara biyo ki Abujan mu karasa a can. Yau dai a takure na ke wlh" dariya tayi sannan tace "yanda na ke jin ka in nan na san gurzu, ina dai fatan ka tanaji dumus dayawa"

Labarin Rayuwata Hikayelerin yaşadığı yer. Şimdi keşfedin