51

602 77 26
                                    

Ta zana jarrabawan, Kuma Alhmdlh komai yazo mata cikin sauki. Sai dai godiyan Ubangiji, don haka suna tsammani sosai a cikin lamarin ga dukkan Wanda ya maida lamuran shi ga Ubangiji. Tana hanyan komawa gida, Kira ya shigo wayan ta. Kai tsaye taji ance mata "Na shigo Kano kina ina ne?" Dif! Natsuwan ta ya dauke, in har kunnen ta ba karya ya mata, to kuwa muryan Zayd taji Yana mata kunnen.

Kai tsaye ta fada mishi inda take jiki a snayaye. Cikin yan mintuna kalilan ya iso wurin, dake shagari quarters zata to akan zoo road su ka hadu. "Bismillah" yace mata, ta bude motan ta shiga. Closest, wurin da zasu iya zama suyi magana in public shine gidan Zoo. Dukkan su basu taba zuwa wurin ba, Amma hakanan suka dukufa wurin.

"Suhaima, Ina neman afuwa a wurin..." Bata bari ya karasa ba tayi saurin katse shi. "Ina zan nemi gafara a wurin ku, tunda nine na zauna daku da wata manufa ta daban" girgiza Kai yayi, yace "Duk da haka Suhaima, zuciyan ki na da kyau. Da badan haka ba, irin wannan Daman da kika samu ba abunda zai hana kiyi amfani dashi ki cutar damu Amma Baki yi hakan ba" ba wai don ta amince ba tayi shiru kawai.

"Tell me about Amal, meya faru da ita?"

"Ba suicide bane" kalman nan da ya fada kadai yayi nasarar sauke wani babban Miki a zuciyan ta, hakan bai boyu ba har Sai da ta saki wani ajiyan zuciya mai nauyi. "Alhmdlh Alhmdlh" ta furta sau biyu a bayyane.

"Me ya same ta?" Ta kara tmbyn shi.

"Cancer ne, bai yi showing kanshi bane Sai da ya fara Kai last stage. Brain turmor ne, in Zaki tuna tana yawan ciwon Kai, Sai Kuma ya hade mata da yawan faduwan da take yi ta sanadiyyan abinda take Sha. To abun ya hade mata ne, harda fatty liver saboda irin nauyin abubuwan da take Sha. Alhmdlh, ta bani sakon da ya min dadi har yanzu nake farin ciki dashi, domin nafi ganin hannu dumu dumu akan mutuwan Amal fiye dake. Ke kam ma ban ganin akwai naki kason ko kadan."

"Taya kenan?" Ta tmby. Dan Kara gyara zaman shi yayi, Yana gyaran murya. "Ta fada min in Miki godiya, domin bayan kun rabu da farko, abubuwan ta cigaba da Sha domin neman gushewan danuwa da bakin ciki. Sai daga baya, da taga sabanin hakan kawai take ta gani, Sai ta fara gwada hanyan da kika daura ta a Kai. In ta daina, Sai ta kasa samun sauki a wancan hanyan nata in ta koma wancan kuma Sai abun ya ragu. Cikin ikon Allah, nakin sai yafi tsaya mata a rai, Kuma Sai ta fi ganin nasara a nan in. Kuma tana kan wannan hanya har lokacin da mutuwa ya riske ta, tace min bata rike ki da komai ba har zuciyan ki, Kuma ita tsakani da Allah take son ki don tana neman afuwa a gunki in ta Miki wani abun" zuwa lokacin, hawaye ne ke yawo kaca kaca akan fuskan Suhaima, hakika tayi rashin Aminiya irin Wanda samun irin ta ke da matukar wuya.

"Lokacin da abun nan ya faru kuwa" Ya cigaba "Lokacin ne farkon da ciwon bata ya fara nuna kanshi. A gaban apartment in gidan su ne, tazo fita ta yanke jiki ta fadi. Shikenan Sai news ya dauka daga saman gidan ta fada saboda Karan faduwan da aka ji da yanayin yanda ta fadin a kife. A daren ranar aka Kira likitan su, ya duba ta Kuma a daren suka bar Nigeria a private jet, kinji dalilin da yasa mu kaje bamu same su ba. Ina Miki albishir da cewa muna kyautata mata samun rahama wurin Ubangiji, don haka addu'an mu take nema a yanzu"

"Allah ya mata Rahma, yasa karshen wahalan ta a nan duniyan ya Kare" Cikin kuka tayi maganan, baki ya dan bata sannan suka cigaba da magana.

Wayan Umar Faroukh ne ya shigo, da sauri ta dauka "An tashi jarrabawa, why are you not at home"

"Ina gidan Zoo" kawai ta fada ya kashe wayan. Da alaman nan in zai zo.

"Shi Zaki aura?" Zayd in ya bukata. Murmushi tayi sannan tace "In Sha Allahu"

"Allah ya yardan mana, Ina Miki fatan Alkhairi Suhaima. Hakika nima yanzu na gane kuskure na, ga hakkin matan da na tabbata Yana bina. Kullum a rayuwata wani sabon jarrabawa nake cin karo dashi. Ina fatan cinye su duka, naga canji wurin Nainerh Kuma nasan daga wurin ki ne, don haka muna godiya"

Labarin Rayuwata Where stories live. Discover now