Arba'in da bakwai

269 53 10
                                        

A hanyar fita daga kotun, Suhaima suka hadu da Nainarh. Kallon kallo su ka tsaya yi ma juna kowa ya rasa abun fadi.

"Suhaima" Nainan ta fada cike da abubuwa dayawa daga sautin muryan ta.

Kafin ta hado abinda za tace mata back, taji Dr Fahad yana fadin tazo su wuce. Gabadaya su Engr murna suka dinga taya su. Abun mamakin kuwa wai harda Faroukh. Ikon rabbi kenan, ita dai Suhaima ba ta da wani bakin magana.

A hanya take fadawa Dr Fahad Anty Nainah ce ya gansu a tare. Shi kanshi Sai da ya jinjina abun.

Ranar wani irin kwanan farin ciki tayi duk da in ta tuna ita tayi sanadiyyan Amal Sai taji wani iri a ranta. Za taso taga zayd, tana bukatan ya mata bayani dayawa game da ciwon Amal in. Duk da dai ta riga ta tafi, yanzu Addu'a ne kawai mafita. Kuma tana yawan mata sosai, ta kanyi mafarki da ita tana mata murmushi. Duniya kenan, Allah ya sa mu dace.

Washegari Barr ce ma Suhaima yayi kawai tayi zaman ta a gida ba Sai taje ba Amma fir taki zancen. Da ita aka fara Kuma da ita za a gama shi a cewar ta. Hakanan dai suka isa kotun da ta cika makil, cikan ta har ya fi na jiya sosai. Kowa zuwa yayi ya gane ma idanun shi labarin da ya watsu ko ta ina cikin gari.

Kai tsaye Patricia aka nemi ta bada nata bayanin. Da farko fir taki bada hadin Kai, Sai da Alkali ya nemi da a mai da ta cell Sai ranar da ta shirya fadin dalilin da tasa Zayd Shan wannan abun bayan har ya manta ya tafi.

Da dai attack in yayi yawa dole ta bude Baki "Hafeez ya dade yana ce min yana so na, ban San ko wasa yake min ba Amma ni kam yayi min ba kadan ba. Don haka mun kasance yana yawan sani wasu aiki da bai kamata ba a cikin company in Kuma ina yi mishi. Ya kan ce zai min duk abinda nake so in nayi mishi, barin ma da ya gane zan iya yin komai saboda shi. Yace zai iya min komai in dai ya samu abinda ya ke so, I can even be his wife. Wannan dalilin yasa nayi tunanin sa ma shi Oga Zayd poison saboda ina ganin if he is no more, Hafeez zai iya samun duk wani abinda yake so tunda na San burin shi kenan. Am the one behind it but is not my fault. Even the fire, Nina kunna gas in Yana fita da kadan kadan sannan na sa igiyan yin leaking so that I will get what I want" nan take wurin ya dau hayaniya Sai da Alkali yayi magana tukun.

"Are you sure you are the only one behind it?" Nan take ta kara tabbatar. Shi kan shi Hafeez never expects this. Turn out Faree is even using Hafeez to gather Information akan Al-mansur. Abun dai duk kwamacala, Sai dai Alhmdlh da komai ya bayyana.

Nan fa Alkali ya fara yan rubuce rubucen shi bayan wani lokaci ya dago ya fara bada verdict in shi kaman haka "Kotu ta yanke hukuncin danka Hafeez a hannun jami'an binciken tsaro na kasa domin su cigaba da gudanar da binciken su. Kafin nan Kotun na Umartar Kulle Company da ake zaton anyi ta'asan a ciki har zuwa lokacin da za a kammala binciken. Bayan haka kuma, za a kiyasta duk wani al-mundahana da Hafeez in yayi ya biya company kudin shi tare da tara da zama kurkuku na wata biyar da Kuma dama da kotun ta bawa Umaymah tana iya shigar da nata karar akan abinda Hafeez in ya mata. Sai Faree'a da aka ci tara dubu dari uku na mutanen da tayi amfani dasu domin cimma wani manufan ta. Batun Rasuwan Amal da lauyan gwamnati yaso ya daga Kuma, dukkan bincike ya tabbatar da ba hannun Suhaima a ciki don haka Kotu ya wanke ta daga dukkan wani zargi da ake mata. Bayan haka dai akwai taran da suma aka cisu ita da Umaymah na kudirin da su kayi akan Zayd Al-mansur. Shi Kuma Zayd in kotu ya bukaci da ya nemi gafarar duk wata yarinya da ya san ya cutar wa rayuwa, Sai duk Wanda bata hakura ba to tana da daman shigar da karar ta." Bayan ya gama fadin wannan ne ya dago ya kalli jama'an kotun da kyau kafin ya kara maida hankalin shi kan abinda ke gagan shi. "Kaman yanda dokar kasa ta tanada, kotu ta yanke ma Patricia zaman kurkuku na ... A sanadiyyan..." Da karfi ya buga guduman da ke kan table in "This is my verdict, kotuuu"

Ko ta ina Yan jarida kawai kake gani suna kokarin ta yanda za ayi su tattauna da wadanda aka yanke ma hukunci a wannan lokacin. Cike hadda Patricia da ke ta faman zabga kuka tana fadin ita fa taimako taso. Umaymah Kuma Sai faman tmby take ta amsa akan za ta shigar da Hafeez kara ko zata kyale? Murmushi kawai tayi ta shiga motan ta. Rayuwa ta riga da ta nuna mai darasi so ba ta ganin sai ta wani wahalar da kanta da dukiyan da take Shan fama kullum wurin tara su. Bayan haka, she have her own issues to face yanzu haka musamman a yanzu da duniya ta San me take ciki, ta Kuma San asalin ta. Sai dai kowa da irin nashi matsalan don haka bata ganin saboda wannan za ta iya durkushewa.

Labarin Rayuwata Donde viven las historias. Descúbrelo ahora