Rayuwata
Babi na biyu
Ranar Goggo ta zo duba ni, ita ma ba yanda ta ke dake tana fama da ciwon kafa sosai. "Hala na miki laifi ne tunda mahaifiyar ki ta tafi kika daina zuwa guna?" Goggon ta fada cikin harshen fulanci. "Ba haka bane Goggo" na amsa mata.
"To kullum na tmby sai ace min baki ce zaki zo ba"
"Goggo akwai abubuwan da nake yi ne" Harara na tayi tace "abubuwan da yafi zuwa wurina, to ko da wasa kar in kara ji" kallon Anty Yana tayi tace mata "in ma kece ke hana ta zuwa daga yau ya kare kina jina?"
"Ni ba ruwana" Anty Yana ta amsa tana kasa da kai.
"Yana kiji tsoron Allah dai" nan ta ke Anty Yana ta fara kame kame.
Tun daga lokacin aka fara barina zuwa wurin Goggo, INA son tsohuwan sosai, fata na Abbah ya barni In koma wurin ta sai dai ba daman tmby" Tun asali Goggo ta fito son Ummi na akan Anty Yana. A yanda lbr yazo mana, tun farkon aure Anty Yana da Abba, da kyar Goggo ta amince aka yi auren. Kuma daman ance halinka ke siyan maka mutunci. Tuni Goggo tayi watsi da Anty Yana da ta gano halin ta, don sai ta shekara in ba Abbah ya data ba ba taje gaida Goggo ba. Ko da Abbah ya tashi auren Ummi, sosai Goggo tayi na'am da zancen ganin Ummin bafulatana ce. Sai do Kowa ya shaida halin irin nasu da ya banban ta ne ya sa hakan.
Wani ranar juma'a munje wurin ta, tunda mu kaje na lura tana ta kallona, ko dan ganin yanda ban saki jikina cikin yan uwana bane, oho. Sai dai ta bari su Adda Falmata sun bar gun ta jawo ni har dakin ta. "Ke lafiyan kuwa? Ko da wani da ke damun ki ne?" Cikin inda inda nace mata "lfy kalau Goggo kin ga wani abu ne?" Hade rai tayi tace "ke dai Wlh kinji kunya shegen tsoro kaman ba Aeey bace ta haife ki, Allah en shamtata an kam"
Ni dai bance mata komai ba, sai fada ta ke yi a cewarta wai na rame sosai. Ko da mu ka tashi tfy gida cewa tayi ba inda zani. "Bari baban naku ya dawo dole in San abinda ake ciki" wani irin kallo na ga Adda Falmata na bina dashi, ni dai duk tsoron abinda zai biyo baya nake. Har rokon Goggon nayi ta bar ni na koma, maimakon hakan rankwashi na tayi ta maida ni cikin dakin ta.
Ranar ko nayi kwana dadi ba wani fargaba a ciki, ko da na tashi da sassafe na riga na saba da aiki don haka tuni na hau yi wa Goggo aikin gidan ta gabadaya. Ko da ta farka taji dadi sosai sai cewa ta ke "Ayyah ai da kin bari su ..
"Goggo me za a dafa miki?" Na tmby duk ba wai iya girkin nayi ba, banda su jajjage da nake yi sai gyaran kayan miya da su alayyahu. Harara na tayi tace "ke yanzu har wani aiki kika iya?" Marairai ce mata nayi nace "Goggo toh ba sai in koya ba" dariya tayi tace "to ai ni ba ma abun kari a gidan nan, daman dumame ne da shayi. Ke dai bara su Ajiddah su shigo su samo miki Kosai da fanke ko kuma Za kici danwake ko doyon da kowan fulawa" wai, na manta rabon da naji ana tmbyn me zanci, daman yawanci a garinmu siyan abin karayawa ake yi. Ko kuma a dinga hadawa, kuma ma sha Allahu ma su saidawan sun iya ga arha gashi kuma ba ha'inci.
Ko a gida yawancin siya ake yi sai dai sai abinda sadiya su ka rage ne ake dan bani shima ba kullum ba. In ko anyi a gida, ba wanda ya damu naci ko kar naci, sannan in ana yi ba zan iya zuwa ince a bani ba na jawo wa kaina magana, sai dai in an gama in lallaba inci a kitchen in.
Gidan Goggo gida ne irin na zamani, sashe kusan uku ke ciki daya nata dayan kuma kishiyan ta ke ciki sai dayan autan Aidah (kishiyar Goggo" da yayi aure nan ya kawo matar shi. Dukkan su biyun da yan uwan su su ke zaune, barin ma Goggo da musamman ta ke sawa a kawo mata yaran Yan uwan ta su zauna tare. Yanzu haka mata biyu ne a gidan sai dai dukkan su sunyi aure sun fito.
![](https://img.wattpad.com/cover/150148529-288-k932188.jpg)
YOU ARE READING
Labarin Rayuwata
General Fiction"Believe me ba wani abun birgewa a labarin Rayuwata shi yasa na gwammaci mutuwar akan Rayuwa irin wannan" idon ta a bushe karoro ta ke maganan ba alamun kuka ba wai don kukan ba Zama dole ba Aa, ta gaji da kukan ne saboda Bai da amfani a gareta do...