Arba'in da biyar

250 59 6
                                        

Rayuwata

Babi na Sha takwas.

Dole Sai a kwana na ukun ne na iya Kai wani abu baki na, shi inma ruwan shayi ne. A bakin Adama nake jin irin raman da nayi, fada take yi wai ban yarda da kaddara bane da bazan fawwala wa Allah lamari na ba. Sai dai banga laifin ta ba a wannan lokacin saboda Adama bata taba fuskantan daya daga cikin matsalolin da na gani ba. Na dade da sanin rayuwa ta bata da wani mahimmanci, tunda na taso ma fuskanci mahaifiyar da ta haife ni ma ta tafi ta barni cikin gararin rayuwa hannun wadanda basu damu dani ba.

Bansan Ya akayi Umar Sanda yazo ba, Amma dai naga shigowar shi tare da maigidan Adama. Ban yi wani mamakin zuwan nashi ba, saboda a halin da nake ciki ba wani abun girgizan da zai shudar da mutuwar Goggo a raina ba. Gaisuwa suka min suka tmbyn ya jiki, duk dai a takaice na amsa musu.

Ina ga alluran cin abinci likita yasa aka min saboda shi kadai ne dalilin da zai sa naji ina jin mahaukacin yunwa. Duk da haka ban wani kula yunwan ba, banda uban fruit da abun ruwa dana dinga durawa ciki na. Shi inma a sanadiyyan nasihan da Umar Sanda ya zauna yayi min, Wanda ba shakka ba karamin ratsa ni yayi ba.

Ranar throughout yana asibitin, motsi kadan zaka ganshi ya shigo. Ina jin Adda Falmata na bala'in wai wani munafunci ne ya kawo shi wurina, daman an bata lbr. Kala ban ce mata ba, don na rasa dalilin zuwa wurina asibiti da take yi. Yaya Baba dai banda shi a maidugurin ma, naji dadin hakan saboda ba wanda naki jini a rayuwa irin shi, tabbas shi in wani irin dafi ne da ganin shi kadai zai ma mutum illa.

A daren ranar Umar Sanda yazo min Sallama, akan wani batu ya taso mishi a Abuja, dole gobe ya ke kafin ya koma Egypt. Nasihan dai ya kara min sannan ya wuce tare da sanar min zai turo min sako ta waya.

Hakanan aka sallame ni a asibiti, na koma gidan Baffah cikin da tunanin wani irin rayuwa zan afka a wannan karon. Ganin ni kadai ne a gidan yasa baffan yace in koma side in Uwargidan shi na zauna. Haka ko aka yi, ba wani abinda ke hada ni da ita banda gaisuwa. Daganan ba ta damu da mai naci ba ko ina na kwana. Ko bata ganni ba, ba abinda ya shafe ta. Har ma gwara dayar matan in bata ganni ba zaka ji tana wai Suhaima kwana biyu kaman bata gidan nan. To tun farko basu dauke ni wata tsiya ba balle in wani girmama su sosai. Duk da haka dai nayi Amanna zaman gidan yafi zama gidanmu dadi ta kowani sashe. Tunda su ba aiki suke sani ba ko aika ko wani wahalan ba. Kawai dai kowa na rayuwan shine.

Da aka koma makaranta Abbah ya turo min kudi na biya registration and all. Accommodation Kuma kudin hostel ya bani, Sai dai faree'a ta nemi da mu Kama wuri nan cikin makarantar kawai mu zauna. Tunda wajen ba security, saboda haka nan staff quarters muka samu wuri muna zaman tare. Zuwa yanzu halin ta ya lalace, ban mata wani wa'azi saboda ba dauka take ba. Takan ce kowa rayuwan da ya zaba ma kanshi zai yi, don haka ita nan ta fuskanta. Na dade da sanin tana bin maza, bi ma'ana runs take yi. Takan ce min ni naga ina da hanyan samun kudi ne Amma ita ba ta da wani da ya wuce wannan in. A lokacin kam Sam bata wasa da Sallah, abinda na jinjina mata kawai kenan. Akan ce ka guji aboki batacce, Sai dai ni a wannan lokacin ina ganin soyayyan da take min ya take komai sannan Kuma ban ganin za ta iya canja min ra'ayi. Babban kuskuren da nayi kenan.

Domin dai a hankali a hankali rashin gata na ke kara bayyana yayin da rayuwa take cigaba min. Abbah ba irin mutum bane wanda ya damu da yaran shi sosai, zai dai sauke muku hakkin makaran ta daganan Kuma sauran Sai anyi da kyar. Duk bayan kwanaki dai zai turo min kudi Sai Kuma in ni na Kira in gaishe shi.

Da farko mafitan da na fara gani shine yakama ta in bi aure ne. Sai dai duk yanda mutane ke fada min Umar Sanda na so na, har yau bai taba furta hakan ba. Ban da maganan karatu Sai Kuma makudan kudin da ya kam turo min da sunan wani ke sa shi. A hankali na fara jan hiran mu a waya kaman yanda ya kanyi ko zan samo mafitan a nan Sai dai bai wani nuna komai ba. Zai dai bani lbrn abinda yayi ranar da Kuma irin rayuwan da yake fatan gina wa kanshi a gaba. Kullum dai kara daure min Kai yake. Ban fadawa Faree'ah ba saboda bata nan, Adama Kuma she is not an option to me don haka direct na Kira Ajiddah.

Labarin Rayuwata Dove le storie prendono vita. Scoprilo ora