Arba'in da biyu

257 57 12
                                        

Rayuwata

Babi na sha biyar

A motan shi mu ka tafi har garin Maiduguri. Ya kaini har cikin gidan Baffah. Hatta kafa na ma da kyar na ke taka ta, ga magunguna kala kala daya hada ni dasu. "Ki kulla da kanki Dam Allah Suhaima,  da kuma dukkan abinda nurse in nan tace miki. Bakomai, Allah na nan sannan ina so ki cire damun da nake ganin kin sa kanki a ciki"

"Damuwa dole ne? Duka duka shekaru na nawa ne a duniya? Amma kasan abubuwan da na fuskanta wani tsohin ma har ya gama rayuwan shi ba zai taba ganin irin su ba" Hawaye shara shara ke zuba a idanuna yayin da na ke magana "Ballantana kuma yanzu da gabadaya rayuwan tawa ma bata da amfani?" Da rudu sosai a fuskan shi ya ke kallona "Ba zan ce kiyi hakuri ba suhaima saboda ina jin baki cancanci wannan kalma ba. Ba a wurina kadai ba, har a wurin kowa ma. Abinda zan ce miki kawai kuma shine, Allah na nan kuma ya san dake" yana fadin haka ya shiga mota yana kokarin tayarwa. Da kyar na iya tsaida shi "Ka gaida Goggo Dan Allah" Hakanan ya bini a baya har zuwa dakin da take zaune. Ina ganin ta na ruga da guda na duk da ciwon da kafafu na keyi, na shige jikin ta. Sai da kuma na shige jikin nata na ji alamun ba karamin ramewa tayi ba. Rudewa nayi in tmbyn ta ba'asi, ba ta amsa ni ba sai datijjuwan matan da ke dakin wacce na gane an kawo tane saboda ta kula da Goggon. "Au Goggona zo da bako bara ya shigo ya gaishe ki"

"Siriki kika kawo min?" Abinda ya fara fitowa bakin ta kenan. Sai da na danyi dariya sannan nace "Aa dan layin mu ne a sabon fegi" ba dai tace komai ba, har Ummar sanda ya shigo su ka gaisa. Har kyautan kudi kuwa ya mata sannan ya fita. Goggo ko taji dadi, dan ita ba dai son mutum mai kyuta ba saboda ita ma gwanace wurin kyautan. Tayi ta sa mishi albarka, sai ce min tayi "Ba zaki je ki raka shi ba?" Ban ce komai ba, haka kuma ban fitan ba har naji tashin motan shi ya wuce. Daganan kullum Goggo sai ta tmbyni gane dashi, ni kam share ta nake yi na kauda zancen. Dan nasan ba wani abinda zai iya taba shiga tsakaninmu dashi a wannan lokacin.

Ba laifi duk da ana yawan zuwa asibiti amma jikin nata yana dan sauki, Alhmdlh. nima naji sauki, saboda duk maganin da aka bani sai da na shanye haka na dinga gasa kaina ina kuka ina zuba Allah ya isa, don har duniya ta kare ban jin zan taba iya yafe ma wadanda suka min wannan abun. Musamman Yaya Baba dashi ne silan komai. In sha Allahu nasan sai sin ga karahen su tun a duniya ma.

Sanda aka koma makaranta ba karmin Dramamu kayi da Abbah ba. Duk dagewan shi, na nuna mishi da in koma Nana Aisha na gwammace in mutu banyi makaranta ba. Goggo ne ta tilasta shi, dole aka siyan min foam in El-kanemi Maiduguri.  Haka kuma na fara rayuwa ta a garin Maiduguri, Borno wato birnin Yarwa. Ba laifi rayuwa gidan ya fi na gidan mn sau dubu duk da ko na san saboda Goggo ne abubuwan suka zo min da sauki, to gashi itama fama take. Rayuwa dai gatanan kawai ne, yau dadi gobe akasin ta. Ban wani samun matsala a makaranta saboda ina jin cewa banda matsalan ind dai ta fannin karatu ne. Ga kuwa dalibai masu kwazo ne sosai aka tattara a makarantan. Haka kuwa muke fafatawa son duk da abinda Mai Aliyu yayi sanadi na katse min dukkan wani mahimmancin rayuwa. Ban jin zan iya hakura da karatun likitanci, ko dan ceton mutane dayawa daga cututuka da kuma taimakon Al'umma musulmi.

Wataranar Asabar aka wayi gari da bakin ciki hade da jimamin babban rashin da aka yi na Inna, abokiyar zamn Goggo kuma mahaifiyar mijin Aunty Amarya. To lamarin Ubangiji kenan, duk da tana fama ita ma dajiki wanda tsufa ne ya jawao amma ko kusa ba za a hada ta da abinda Goggo ke ji. Amma da ke lokaci yayi, ko ba ciwon tafoya za ayi. Goggon kuwa ta ji mutuwan sosai. Musamman su mutanen da, duk da ba za ace ba a taba samun sabani ba, amma kuma anyi zaman mutunci. Duk da ciwon kafan ta hakanan ta sa su Abba da Baffah a gaba sai da suka hakura suka kaita Damaturun. Har aka yi zaman gaisuwan kwana uku, sai daida ka ganta kasn abun yana damun ta sosai, karshe dai ciwo ya tashi gadan gadan kuma shi yayi sanadiyyan komawan mu Borno ba shiri. Abinda ake gudu kam hakanan sai da ya faru. Wannan lokacin ma ba karamin jinya tayi a asibiti ba, da ka ganta kasan tan jin jiki. Ni kam duk lokacin da tayi irin wannan ciwonba karamin damuwa nake ba, kai hatta yanayi na bai boye hakan har wani irin rama na daban nake. Na riga na san ita ce gata na a duniyan nan, kuma raahin ta ba karamin girgiza ni zai yi ba. Sai dai alamu na yawan nuna ban da wani zabi a rayuwa kuwa.

Labarin Rayuwata Onde histórias criam vida. Descubra agora