*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*MUTANEN DIJE K'ARANGIYA INA GAIDA KOWA A KOWACE NAHIYA KUKE CIKIN DUNIYA ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU, HADIZA D/AUTA TANA GODIYA SOSAI👍🏻*
*Lamba ta 16*
Maigari ya yi wani mere ya mayar da kai gefe alamun rashin gamsuwa da zancen Liman, ganin haka yasa Liman d'in ya gyara zamanshi yace
"Ni a tawa shawara abunda naga yafi a kira MALAM Sanda a sanar dashi zancen, ka ga duk abunda ya fad'a shikenan da shi za muyi aiki"
Maigarin ya yi shiru na d'an lokaci sannan yace,. "To za mu kirashin duk yanda muka yi zaka ji yarona, amman ina son ka yi nazarin maganata kafin ka yi nutso cikin abunda zaka zo daga baya kana cizon yatsa, Sabida a zahirin gaskiya yarinyar nan kirin jijiya ce, bata jin magana ko kad'an ina ji maka tsoron ka je da ita cikin danginka ta wargaza maka zumunci da Yan uwanka"
Lawi ya kara sunne kanshi cikin sanyi murya yace,. "Ai yanzu kurciya ce Baba jikina yana bani zata natsu matuk'ar ta ga bata gaban Iyayenta"
Maigarin ya d'age kanshi a sama yace,. "Uhm lalle kam akwai k'urciya to ALLAh ya baka k'arfin gwiwar tunkarar matsalolinta"
Lawi ya washe Baki fuska a sake yace,. "Ameen Baba na gode ALLAH ya rufa asiri kuma ya ja da nisan kwana"
Maigarin da Liman suka ce "Ameen" Lawi ya mike tsaye yace
"Ni zan dan fita babban birni in yo muna siyayya"
Maigarin yace "a dawo lafiya ALLAH ya tsare"
Suka yi sallama Lawi ya tafi zuciyarshi cike da farin cikin ganin cewa tamkar ma Dijen ta zamo Matarshi, bayan tafiyarshi ne Liman ya yi ta fahimtar da Maigarin akan fa'idar auren Dije birni, amman Maigarin kam sanin wacece Dijen yasa sam yak'i gano abunda Liman yake son nusar dashi, sai dai ya aika a Kira masa Baffahn Dijen don ya ji ta bakinshi saboda shi ya sa a ranshi ba zai tab'a yarda ya yi tsanin abunda za'a zo daga baya ayi kuka dashi ba.
Aiko dan sak'on yana sanar da Baffah'n Dije bai yi k'asa a gwiwa ba ya garzayo cikin fad'uwar gaba domin ya ji kiran me ne Maigarin ya ke masa kuma yanzu, duk da wani gefe na zuciyarshi yana sanar dashi cewa Dijen ce ta sake aikata wani abin bayan sakawa D'anbirni turaren mayu da ta yi, don duk iya b'oyon da yayi akan kada a gano Dijen ce sai da Maigarin ya gano itace, don kai tsaye ya kira Baffah'n ya yi masa Kamar daman cen ya san itace d'in, ta sigar bugun ciki yace da shi,
"Sanda mai yasa 'yarka bata bari a zauna lafiya ne wai? abun ya wuce kanmu ga shi yanzu har ta fara tab'a bak'inmu, to WALLAHI wannan karon za ta janyo maka zama gidan kaso matuk'ar baka tsawatar da ita ta ajiye shirmenta da rashin hankalin da take yi a garin nan ba"
Baffah jikinshi ya d'auki rawa ya fara cewa,. "Don ALLAH ayi hak'uri WALLAHI na yi mata fad'a sosai akan wannan abun da ta aikata, kuma yanzu haka ma an samu ta rage duk wani k'irin ji da take yi, insha ALLAHu hakan ba zata sake faruwa ba"
Maigarin ya yi shiru sannan yace, "au! Ashe dai da gaske itace d'in ce ta aikata? Um lalle rashin mutuncinta sai hauhawa yake yi, to WALLAHI bari kaji ta sake kwatanta wannan shirmen a gaban kowa zan saka Bafade ya yi mata d"an banzan duka a garin nan sai ya farfasa mata jikinta duka WALLAHI ka ji na rantse kuwa "
Cikin fushi ya mike ya shige cikin gida sai Liman ne ya dinga fahimtar da Baffah'n akan abun da Dijen ta yi bata kyauta ba, Baffah sai hak'uri kawai yake ta badawa cikin sanyin jiki ya baro k'ofar Gidan Maigarin.
To shiyasa yanzu ya ji tsoron wannan kiran kuma da Maigarin ya sake yi masa, a sukwane ya isa ya zauna cikin d'ar d'ar ya fara mik'a masu hannu suka gaisa, sannan cike fargaba ya ce

YOU ARE READING
DIJE ƘARANGIYA
Genel KurguLabarine mai cike da barkwanci tare nishandarwa da fadakarwa a fakaice don kuwa zai saka mai karantashi ya ƙyaƙyata har ma ya faɗo kan gado ba tare da ya san yayi ba saboda dariya zai saka mutumcikin farin ciki marar misaltuwa.