67

348 24 0
                                    

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*

*NA HADIZA D/AUTA*


*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*

*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*

*Lamba 67*

Zancen Safwan ya tabbata don kuwa sati biyu bai cika ba Dije ta fara laulayi mai ɗan karen zafi, don kuwa ruwa ma idan ta sha sai ta amayesu, ga shi a lokacin Safwan ya fara zirga zirgar neman aikinshi, inda aka yi dace aka nemeshi Abuja interview, shiyasa ya mayar da ita wurin Hajiya amman ko da yaushe suna maƙale a waya har ALLAH ya dawo da shi, sannan ya kwashi Matarshi suka koma gida yana ci gaba da renon abarshi, don kuwa duk abunda take so baya jin nauyin dattijuwar da ke taya Dijen aiki yake zagewa kitchen ya yi mata, ko ba daɗi ta cinye tana santi daga baya kuma ta amaye tass!, Haka suke abu ƙaɗan ya ce sai sun je Asibiti an dubata don baya son ta zauna cikin gida da wata matsala a tattare jikinta, shiyasa duk wani abu sai ya nemi sani tare da shawarwarin ƴan Asibitin, duk da wani zubin yana biyewa son zuciyarta ya yi mata duk abunda ta ke so saboda kawai ta yi farin ciki, don ba ƙaramin jin jiki take yi ba, cikin haka ne Safwan ya tura direba ba tare da ta sani ba ya ɗauko su Baffah da Inna da Hansai da Usmanu don Gambo ta ce ita ta yi tsufa ba zata iya yin wannan doguwar tafiyar ba, duk da har a ranta ta so ace ta je ta dubo jikallenta, amman yanayin jikinta na tsufa yau lafiya gobe ciyo yasa ta haƙura ba don tana so ba.

Dije cike da mamakin ganin gidan wasu ƴan'uwansu Safwan da su Surayya a kitchen sai hidimar dafe dafe da soye soye suke yi, in sun sauke wannan su ɗora wancen gida ya runtume sai zuba ƙamshin garar da ake ta haɗawa su Inna ake yi, duk abunda aka yi sai an kawo mata ace ta ɗanɗana ta ji in ya yi, cike da mamaki take tambayarshi wai halan wasu baƙi ne zai yi masu muhimmanci shiyasa ake ta wannan hadahadar?, Yana dariya ya ce

"Ke dai ki ci ki ƙoshi ki sha maganin amanki ki je ki yi wanka ki tsalo kwalliyarki cikin  sababbin ɗinkunanki"

Cike da jin daɗi ta fara cin wani dambun nama tana ci tana kaɗa kai alamun ya yi daɗi sosai, hannunshi riƙe da plate ɗin tana ci yana yi mata dariya, bayan ta ci abunda zata iya ci ne ya bata magani ta sha sannan ya je ya taimaka mata ta yi wanka, wanda ko shi ɗin sai da suka ɓata lokaci sosai sunata wasarsu ta ma'aurata, tare suka yi wankan suka fito sannan suka shirya cikin taimakekeniyar juna, kafin ka ce me sai ga su dukansu sun fito shar! Abunsu kowane sai tashin ƙamshi yake yi, duk da ta yi rama amman hakan bai hana kwalliyar ta yi kyau ba, don kuwa fatarta ta washe sosai ta yi haske dai dai jikinta, haka ma ta ƙara yin kyau masha ALLAH dukiyar fulaninta sun ƙara cikowa sosai a ƙirjinta, waɗanda a kullum baya gajiya da lalacewa akansu yana santin yanda suke ta ƙara hawa tamkar an hura masu iska ga taushi tamkar balombalom, dole ba don ta so ba take sakin jiki ta barshi ya yi abunda yake so don duk da ciyon ta wannan ɓangaren baya ɗaga ƙafa, a cewarshi wai duk wani maganin da zata sha bai kai wannan tasiri a jikinta ba, da wayo da lallami yake samun abunnda yake ƙulafuci, don idan ma ta ce zata yi tirjiya ma ba haƙura zai yi ba shiyasa take ta danne zuciyarta tana faranta masa, amman ita sam bata son damuwa a wannan lokacin da zai barta na tsawon watanni da tafi sha'awar hakan fiye da yanda yake manne mata akan biyan buƙatarshi.

Bayan sun gama kimtsa komi da ko'ina ne Safwan ya kawo falo ya ce ta zauna ta jirashi minti biyar kacal zai je ya tarbo baƙinshi ya dawo, aikuwa cike da mamakin da son ganin waɗanni baƙi ne haka?, Ta zauna tare da su Surayya suna kallo a falo suna fira jefi jefi, don ko ita ya ja kunnenta sosai akan kada ta sanarwa da Dijen zuwansu Baffahn ya fi so ta gansu unexpected, ai kuwa suna nan suka ji saukar motoci, Surayya ta yi tsalle ta kalleta ta ce

DIJE ƘARANGIYAWhere stories live. Discover now