*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*Lalle yau kwalliya ta biya kuɗin sabulu💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 yasin yau kun faranta man fiye da tunaninku🥰 don haka ga nawa tukuici nan gareku masoya Dije Ƙarangiya all, ku ma ku ji daɗi kamar yanda na ji, ku daɗe ku yi lasting mutanena gaba ɗayanku ina yinku sosai ba shakka👍🏻*
*Lamba ta 46*
Safwan mamaki da al'ajabin da ta bashi ne yasashi daskarewa ko motsi ya kasa yi bale ya yi wani yunƙurin kare kanshi, illah kallon Zee da yake yi yana girgiza kai, ganin hakan yasa Fiddo ta yi saurin riƙo hannun Zee tace
"Zo mu je ciki ku gaisa da Hajiyarmu Aunty, wannan da kike gani ba kowa ba ce face ƙaskantacciyar ƴar aikinmu, dubarta da kyau ki gani bagidajiya ce usuli ƴar ƙauyen ƙayau, ta nace akan dole sai yaya Safwan ya aureta bayan kuma shi ko kaɗan baya sonta"
Ta janyo hannun Zee ta yi wa Dije wani kallo ta buga mata ƙaton tsaki tace, " mtsss! Mayya kawai"
Zee tana yi tana waigenshi zuciyarta cike da ƙunar baƙin cikin da Dije ta sakar mata, sai wassafa yanda zata shaƙe Dijen take yi a ranta har sai ta ɗauke numfashi sannan ta saketa, har suka isa ɗakin Hajiyar suka zauna bata san ma sun je ba, sai da ta ji Fiddo tana gabatar da ita ga wata Auntynsu sannan ta dawo hankalinta ta fara sunne kai tana gayar da su.
Safwan kam shigewar su Zee ciki yayi dai dai da dawowar natsuwarshi, ya kai kallonshi ga inda yake tsammanin ganin Dijen sai dai kuma wayam bata nan, ya wara idanuwanshi a masifance domin ya hango ta ina zai ganta ya sauke fushinshi akanta, sai dai kuma bata ba dalilinta a falon duka, a harzuƙe ya yi wurin Surayya yace
"Ina magen yarinyar cen ta tafi???"
Sury cikin firgici tace
"WALLAHi Ni ma bansan inda ta je ba yayanmu"
Safwan ya kaiwa iska duka sannan ya bar wajen ya sake dawowa ya ce da ita, "to ki yi gaggawar dubo man ita yanzun nan idan ba haka ba WALLAHi yau daga ke har ita sai kun san dani kuke zance"
Cikin rawar jiki Surry ta miƙe ta yi ɗakinsu domin ta gani Dijen tana cen ko kuwa, sai dai ta duba ko'ina Dijen bata gidan take ta sanar da shi yana huci ya yi wurin Hajiya, sai dai tuno ɗakin da mutane yasa ya ja ribas dole tare da furzo iska mai zafi a bakinshi yana wani bubbuga kanshi alamun ta saka shi a tension da yawa.
Yana nan tsaye sai ga Fiddo ta fito tare da su Zee tana ganinshi ta yi saurin zuwa wurinshi tace, "big bros WALLAHi yau idan ka kama yarinyar nan ka ci ubanta da kyau da kyau, don ni kaina yau sai na tayaka mun ci uban shegiya......"
Kallon da Safwan ɗin ya yi mata ne yasa ta yi saurin cewa da su Zee "Aunty ku zo mu je ku ci abincin kafin mu je wajen da za'a yi event ɗin"
Zee ta yatsina fuska ta kalli Safwan tace,
"Barshi kawai Ƙanwata ni yanzu ma zamu koma gida"
Safwan ya yi saurin zaro ido cikin wani sabon tashin hankali ya marairece fuska yace, "Sorry Unique ke ma kinsan ke ce dream ɗina safe da rana, ke ce wadda nike mafalkin aure a kowane lokaci, wannan yarinyar ba kowa ba ce a wurinmu face ƴar aiki kamar yanda kika ji Fiddo ta sanar da ke tun farko"
Zee ta yi masa wani arnen kallo mai cike da ma'anoni sannan ta nufi hanyar fita ƙawarta ta riƙo hannunta, cikin wayancewa ta ce da Fiddo mu je ki kaimu wajen da za'a yi bikin, Fiddo cike da damuwa ta ce "to ku yi haƙuri ku ci abincin mana kunga kun kwaso tafiya ga shi ko ruwa ma baku sha ba"
Ƙawarta Ruma ta yi murmushi ta ce "ok to mu je mu ɗin ai sai mu yi sauri mu kammala"
Fiddo cike da jin daɗi ta kai su ɗakinsu da ta riga da ta shirya shi tsaf saboda tarbonsu, ta nuna masu toilet sannan ta fito zuwa kwaso masu kayan abincin, Safwan da ke tsaye jiki ba kuzari damuwa fal ranshi yace

YOU ARE READING
DIJE ƘARANGIYA
Fiksyen UmumLabarine mai cike da barkwanci tare nishandarwa da fadakarwa a fakaice don kuwa zai saka mai karantashi ya ƙyaƙyata har ma ya faɗo kan gado ba tare da ya san yayi ba saboda dariya zai saka mutumcikin farin ciki marar misaltuwa.