*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Aski ya zo gaban gashi Mutanena💃🏻*
*Lamba 70 *
Haka dai suka kwana ba natsuwar zuciyoyi, bayan SALLAHr Asuba Safwan ko da ya dawo masallaci ya taradda Zee tana ta karatun Qur'ani, abun ya buregeshi kuma haka ya ba shi mamaki sosai, saboda sanin da ya yi mata ada da ƙyar ma take tashi yin SALLAHr a lokacin, sannan idan ma ya matsa mata ta yi tana kammalawa take yin kwanciyarta ko addu'ar kirki bata tsayawa yi, amman yanzu ita ce har da su karatun Qur'ani, cike da jin daɗin sauyin da aka samu ne ya zauna kan gadon yana ƙarasa addu'o'inshi na azkar, har bacci ya fara janshi ya kwanta ba shiri saboda baccin da ya fiegeshi ba tare da ya shiryawa hakan ba.
Misalin ƙarfe takwas ya falka saboda ƙamshij abun break ɗin da take haɗa masu, mamaki ya sake kamashi ya fito ɗakin ya nufi kitchen yana kallon yanda take ta hadadarta, cikin shigar wata doguwar riga ƴar kanti, tana ganinshi ta diririce tana gayar da shi cikin ladabi, bayan ya amsa ne zuciyarshi cike da jin daɗin sauyin da ta samu, ya fice kitchen ɗin zuwa sashenshi saboda zuciyarshi da ke ta kwaɗayin son jin muryar Uwargidanshi, don tun yana kan hanyar shigowa garin da suka yi waya ta ji ya sauka lafiya ta kashe wayarta, saboda kishin da ke cin zuciyarta game da zuwanshi wurin Zee, da abun ya kwana a ranshi saboda ya yi ta kiran wayoyinta a kashe ta Husnah ma a kashe, cikin takaici ya kira Aunty Ummi ya ce ta haɗashi da ɗaya daga cikinsu yana son yin magana da Dijenshi, Aunty Ummi ta nuna masa dare ya yi sosai ya dai haƙura sai da safe, saboda a lokacin ƙarfe sha biyu da mintuna dole ba don ya so ba ya haƙura amman zuciyarshi cike fal da son jin dalilin da Dijen ta aikata hakan.
Shiyasa ko da ya shiga sashenshi ko wanka bai yi ba ya fara nemanta a waya, aka yi da ce ta shiga itama caraf ta ɗaga sai dai shirun da ya ji ta yi masa ne yasa shi saurin faɗin
"Me na yi maki kika horani da rashin jin muryarki?"
Sheshshekar kukan da ya ji ne a kunnenshi yasa ya yi saurin sake wata maganar a rikice ya ce
"Subhanllah me ke faruwa ne? Me aka yi maki? Wa ya taɓa man ke don ya ga bana nan?"
Dije ta sake fashewa da kukan gaba ɗaya cike da ruɗewa ya ce
"Plss babyluv don ALLAH ki daina kukan nan ki sanar da ni abunda ya faru idan har kina son ganin natsuwata"
Cikin kukan Dije ta ce
"Ka gaisheta"
Tana ƙare faɗar hakan ta datse kiran, cikin wani sabon tashin hankali ya sake bi da wani kiran amman har ta tsinke bata ɗauka ba, ganin hakan ya sa ya dinga kiran Husnah kira bayan kira, tana bacci dole ta miƙe ta ɗauka ya ce da ita ta kaiwa Dijen, ta miƙe cike da jin haushin katse mata bacci da aka yi, sai dai kukan da ta tarar tana yi ne yasa jikinta ya yi sanyi, ta miƙa mata wayar ta fito zuciyarta cike da jin zafin kukan da ta ga Auntynta tana yi, don tun jiya take lallashinta akan ta yi haƙuri ta daina kukan da ta ke yi na rashin Auncle ɗinsu, ta yi kamar ta haƙura ashe bata haƙura da kukan ba.
Dije ta kara wayar a kunne tana share hawayenta ta ce
"Ba wani abu fa kaina ne yake ciyo"
Daga cen ɓangaren ya sauke ajiyar zuciya yace, "haba haba My luv to meyasa ba zaki sanar da ni ba kike wahalar man da kanki da Babyna? Yanzu ki shirya Aunty Ummi zata zo ta kaiki Asibiti sannu kin ji? ALLAH ya baki lafiya"
Ta ce "Ameen" cen cikin maƙoshi sannan ya sake cewa "ya kwananki da na Babyna?"
Ta ce "ƙalau"

YOU ARE READING
DIJE ƘARANGIYA
Fiksi UmumLabarine mai cike da barkwanci tare nishandarwa da fadakarwa a fakaice don kuwa zai saka mai karantashi ya ƙyaƙyata har ma ya faɗo kan gado ba tare da ya san yayi ba saboda dariya zai saka mutumcikin farin ciki marar misaltuwa.